Ina yiwa mai karatu barka da Sallah, da fatan Allah ya maimaita mana ganin na wasu shekarun cikin yalwar arziki da lafiyar jiki da zaman lafiya.
Kusan na jima ina yin rubuce rubuce a kan irin abubuwan da kan faru a lokacin da a ke bukukuwan Sallah, ba zan iya tuna takamaimen lokacin da na fara ba, amma ina iya tuna dalilin da ya sa hankali na ya karkata ga bukukuwan Sallah.
A wadancan shekarun babban dalili shi ne; a duk ranar Sallah karama ko babba matasa kan yi gungu (a wasu garuruwan har su dinka kaya iri daya) su je wuraren da a ke yin wasannin sallah. Wurin wasannin kan hada ‘yan unguwanni daban daban, don haka sabani kalilan ya kan kunna wutar bala’in da zai kai ga kisan rai. An yi haka ya fi a kirga. Kamar a Kaduna wuraren da su ka yi kaurin suna a wancan lokacin kan fadace – fadace har da kisa sun hada da; ‘Gamji Gate’ da ‘Galady’.
Haka kuma a washegarin sallah, gungun matasan na sake ziyartan wadancan wurare, inda da zaran an hadu sai kuma a shiga batun daukar fansa, wanda a nan ma wasu rayukan ne ke salwanta. A hankali, wannan al’adar ta zama babba, a kusan garuruwa da daman gaske da ke Arewacin Nijeriya a na aikata hakan.
Sannan abu na biyu wanda ya biyo baya shi ne; matasa sun fara wayewa daga shiga harkokin daba da kauranci. Wannan kuma ya auku ne har da bunkasar wayewa da kuma yawan mu’amala da kafafen sadarwa. Amma sai na sake fahimtar cewa da a ka daina sare – sare a kungiyance a lokutan bukukuwan sallah, sai kuma wata muguwar al’ada ta bijiro, ita ce ta yin wasa da mota ko mashin a wannan lokaci.
A irin wadannan wasanni da mota ko babur a lokutan bukukuwan sallah a kan samu rahotannin rasuwar rayuka da dama daga jihohi har ma da kauyukan jihohin. Wanda wannan babban abin lura ne da damuwa.
Iyaye su ne ke da kaso mafi tsoka a wurin dakile ire – iren wadannan al’adu a lokutan bukin sallah, babu yadda za a yi gwamnati ta iya magance wannan abu ba tare da iyaye sun fara na su aikin ba.
Idan da a ce kowanne Uba zai tsawatarwa dansa cikin nasiha da lalama tare da yi mishi bayanin irin hadarin da ke cikin shiga zugar masu irin wadannan al’adu da za a samu karancin rahotannin barna. Haka kuma idan iyaye za su rika bibiyan mu’amalolin ‘ya ‘yansu a lokutan wannan shagali na Sallah, shi ma zai bayar da daman su iya dakile yiwuwar afkawar matasa ga irin wannan dabi’a.
Wasu iyayen sun yi kokarin hana ‘ya ‘yansu ga shiga harkokin dabanci da kauranci. Amma yanzu babbar matsalar da ke fuskantar al’umma ta girmi dabanci da kauranci, wanda kuma idan Iyaye ba su dauki matakin gaggawa ba, karshenta su ne za a bari da kukan takaici a kuma haifarwa da al’umma da annoba.
Kamar yadda al’amarin fasadin Luwadi ya zama ruwan dare; a wannan lokutan bukukuwan Sallah masu irin wannan dabi’a ta dabbobi za su fake su yi ta bata kananan yara. Kwanakin baya na ke ce ma wani abokina ya kamata mu yi bincike a kan dalilin da ya sa shaidanu ‘yan luwadi su ke farmakan kananan yara.
Idan a shekarun baya al’amarin luwadi bai shigo kasar hausa sosai ba, toh yanzu kam ya shigo ya mamaye wurare da dama. Kusan kullum sai ka ji labarin an cafke wani dan iskan ya na aikatawa. Abin takaicin shi ne kaso 80 da a ke kamawa, su na aikatawa ne da kananan Yara da kuma Matasa.
Tunda mun fahimci cewa wadanda su ka fi fadawa tarkon ‘yan luwadi su ne ‘yan shekaru 7 zuwa 30. Dole ne iyaye su sa idanu sosai a kan duk wani motsin ‘ya ‘yansu. Ba ko ina ya kamata a kyale Yara su rika zuwa ba. musamman ma ya kamata Iyaye su rage yawan yawace yawacen Yara da sunan ‘Yawon Sallah’.
Wannan zamanin ya zo da masifu da bala’o’i iri iri wadanda dole ne sai kowa ya shiga taitaiyinsa tare da daukar matakan kiyayewa. Ba wai ina nufin kar a bar yara su yi ziyara ba, amma a matsayinka na mahaifi ko mahaifiya ya kamata ne a ce kun san ina ne ‘ya ‘yanku su ka je, idan son samu ne ma, ya zama ku ne za ku kai su wurin ziyarar ta yadda za a samu ladan tare.
Na biyu shi ne, akwai wasu kuma wadanda mutane ne amma dabi’ar tamkar ta dabba. Su kuma wadannan, bata kananan yara mata su ke yi; Kaman ‘yan shekaru 5 zuwa 10. Su kan yi musu dabaru, tare da jan hankalinsu da sunan goron sallah. Saboda haka, a nan ma dole ne Iyaye ya zama sun takaita yawon ‘ya ‘yansu mata, saboda gudun sharrin dabba a rigar mutum.
Na uku shi ne yadda samari da ‘yan mata su ke yin amfani da lokacin sallah a matsayin ranakun da za a aikata zina ce zina ce da masha’a. Iyaye na da karfin ikon hana afkuwar wannan masifa, ta hanyar takaita yawace yawacen su ‘yan matan.
Daga karshe zan so iyaye su fahimci cewa; ko dai su tashi tsaye wurin yiwa ‘ya ‘yansu garkuwa daga wadannan mugaye da shaidanun mutane, ko kuma a yiwa rayukan ‘ya ‘yan nasu katoton tabon da warkewarshi sai an yi zufa. Binciken masana halayyar jama’a da zamantakewa ya tabbatar da cewa, idan a ka fara aikata alfashar luwadi da Yaro ya na wahala ya daina. Idan kuma bai daina ba, dole ne zai bata wasu yaran da ya ke rayuwa da su. Idan Iyaye ba su motsa ba yanzu, sai yaushe? Mu hadu mako mai zuwa!
Wannan shafi an samar da shi ne domin watsa rubuce rubuce na ilmantarwa da fadakarwa musamman wadanda su ka shafi IIlmin sanin halayyar dan Adam da zamantakewa (Sociology). Alqalamin shafin zai fi karkata ga rayuwa, musamman na matasa. Sunan shafin ya samo asali ne daga jaridar Leadership Hausa. Shafi ne wanda ke kawo rubuce rubucen marubuci Sulaiman Bala Idris (ISB DAURAWA) +2347036666850
Friday, 25 September 2015
Friday, 18 September 2015
Hadarin Da Ke Cikin Killace Yara
Tabbas rayuwa a tare da mutane wani babban al’amari ne mai muhimmancin gaske ga dan Adam, wannan ba ma ga mutane kadai ba, hatta Birai su na da bukatuwa ga rayuwa tare da ‘yan uwansu a matsayin al’umma.
Binciken ilmi da wasu masana halayyar dan Adam da zamantakewa Harry da Margaret Harlow su ka gudanar a shekarun 1962 da 1977, sun fitar da bayanai masu tasirin gaske dangane tasirin mu’amala a tsakanin dabbobi.
Masanan sun gudanar da binciken ne kamar haka: sun dauki jiriran Birai biyu daga wurin mahaifansu inda su ka kebe su a cikin keji daban daban. A kowanne keji akwai kirkirarrun Birai guda biyu a matsayin iyayen wadannan jarirai, akwai sakago (Biri mara rai) wanda a ka kera shi ta hanyar sanya abun tsotso ‘Feeding bottle’ a jikinshi. Sannan kuma akwai wanda a ka kera shi a ka lullube shi da irin jikin Biri amma babu wannan abin tsotso a jikinsa.
Binciken ya tabbatar da cewa jariran Birai din su kan haye kan kirkirarrun Iyayensu wadanda a ka kirkire su da irin jikin asalin Biri su kwanta har sai yunwa ta ci su, sai su sauko su nufi wurin dayan kirkirarren Birin da ke dauke da abin tsotso su sha idan sun koshi sai su koma saman wancan.
Bayan watanni shida da a ka fitar da wadannan Birai a ka hada su da ‘yan uwansu, sai ya kasance wannan tsawon lokaci da su ka dauka a kebe ya taba su, ta yadda a ko da yaushe sai dai su koma gefe su na kallon yadda sauran Birai ke gudanar da al’amuransu na yau da kullum ba tare da shiga ba. dalili kuwa shi ne wadannan Birai sun yi wayo ne a kebe, ba su samu damar koyon yadda a ke mu’amala da sauran ‘yan uwa Birai ba.
Da wannan dan takaitaccen misali wanda na dora shi a bisa binciken ilmi na ke son tabbatarwa cewa shi Mutum ya fi Biri bukatuwa zuwa ga koyon mu’amalolin yau da gobe.
Al’amarin killace Yara kuwa wani abu ne mai girma, duk da ya ke babu yadda za a yi don kawai a na so a fahimci me zai iya faruwa idan an killace su, sai masana halayyar dan Adam da zamantakewa su debi Jarirai su killace su a matsayin gwaji. Amma daga bincike da a ka gudanar dangane da irin sakacin da iyaye ke yi ko kuma wadanda a ke dauka domin rainon jarirai ke yi, an tattara bayanai sosai dangane da irin hadurrra da ke cikin killace Yaro. Zan yi kokarin kawo misalan binciken da a ka gudanar wadanda a cikinsu akwai darussa da ke nuni da hadurran aikata hakan.
Akwai wata yarinya da a ka haifa a shekarar 1932 mai suna Anna, iyayenta ba aure su ka yi a ka haife ta ba, bilhasali ma mahaifiyarta na da matsalar tabin kwakwalwa, saboda haka tun kafin haihuwarta babu wanda ya damu da ta rayu ko ta mutu. A haka a ka haifi Anna, wacce cikin rashin kulawa da nunawa damuwa a ka killace ta a wani kuryan daki da ke gidan mahaifin uwarta. Mahaifiyarta ta na fita tun da asuba ta tafi gona kuma sai dare ya yi nisa ta ke dawowa. Saboda haka ne Anna ba ta samu kulawa da kauna kamar yadda sauran ‘ya ‘ya ke samu.
Masanin halayyar jama’a da zamantakewa Kingsley Dabis a shekarar 1940 ya yi fashin baki dangane da halin da a ka tsinci Anna a shekarar 1938, kamar haka: (Anna) ba ta iya yin magana kamar yadda dan Adam ke yi, haka nan kuma ba ta iya yin tafiya kamar yadda kowa ke yi, ba ta fahimta don an alamta mata abu da hannu, ba ta iya cin abinci da kanta ko da an ajiye mata abincin a gabanta, sannan ba ta san menene tsafta ko kazanta ba.
Wannan al’amari duk ya faru da Anna ne a cikin shekaru shida a killace. A dai dai wannan lokaci ne a ka sa ka ta a makaranta ta musamman, inda a hankali ta fara koyon yadda a ke tafiya da kafafu biyu, yin magana, da kuma tsaftace kanta. Anna ta na ‘yar shekaru 10 a duniya ta mutu, amma kafin mutuwarta an ruwaito cewa ta koyi yadda a ke bin umurni, yin magana, wanke hannayenta biyu, goge bakinta tare da kokarin taimakon wasu Yaran.
A shekarar 1970 an tsinci wata yarinya ‘yar shekaru 13 mai suna Genie. Ita Genie an tsince ta ne a wani kullallen daki ita kadai tun ta na ‘yar watanni 20 a duniya. Mahaifiyarta ta yi haka ne saboda ba ta son a san ta haihu. Sai ta rika watsawa yarinyar abinci ta tagar dakin. Genie ba ta taba jin sautin dan Adam ba, saboda babu wanda ya taba yi mata magana, haka kuma babu talabijin ko Rediyo a dakin.
Masanan da su ka amshi Genie bayan an tsinto ta sun bayyana ta kaamar haka: a lokacin da a ka kawo ta sam ba ta san wani abu wai shi mu’amala ba. ba ta san ya a ke yin fitsari ko bayan gari ba, ba ta iya cin abinci yadda mutane ke tattaunawa a baki kafin su hadiye ba. ba ta iya rike fitsarinta balle bayan gari. Saboda rashin tauna abincin da ta ke yi a lokacin da a ka tsince ta, girman jikinta da tsawonta bai fi na Yaro mai rabin shekarunta ba.
Da wadannan ‘yan misalai za mu iya fahimtar cewa shi killace Yaro a hana shi mu’amala da mutane babban hadari ne wanda zai jefa yaron cikin sahun wadanda ba su iya mu’amala da mutane ba. kuma wannan rashin iya mu’amala na iya ci gaba da tasiri a rayuwar mutum har zuwa girmanshi, ta yadda za ka ga mutum cikakke amma idan ya kwafso maka wani shirmen sai ka dauka dan firamare ne.
Mu hadu mako mai zuwa
Binciken ilmi da wasu masana halayyar dan Adam da zamantakewa Harry da Margaret Harlow su ka gudanar a shekarun 1962 da 1977, sun fitar da bayanai masu tasirin gaske dangane tasirin mu’amala a tsakanin dabbobi.
Masanan sun gudanar da binciken ne kamar haka: sun dauki jiriran Birai biyu daga wurin mahaifansu inda su ka kebe su a cikin keji daban daban. A kowanne keji akwai kirkirarrun Birai guda biyu a matsayin iyayen wadannan jarirai, akwai sakago (Biri mara rai) wanda a ka kera shi ta hanyar sanya abun tsotso ‘Feeding bottle’ a jikinshi. Sannan kuma akwai wanda a ka kera shi a ka lullube shi da irin jikin Biri amma babu wannan abin tsotso a jikinsa.
Binciken ya tabbatar da cewa jariran Birai din su kan haye kan kirkirarrun Iyayensu wadanda a ka kirkire su da irin jikin asalin Biri su kwanta har sai yunwa ta ci su, sai su sauko su nufi wurin dayan kirkirarren Birin da ke dauke da abin tsotso su sha idan sun koshi sai su koma saman wancan.
Bayan watanni shida da a ka fitar da wadannan Birai a ka hada su da ‘yan uwansu, sai ya kasance wannan tsawon lokaci da su ka dauka a kebe ya taba su, ta yadda a ko da yaushe sai dai su koma gefe su na kallon yadda sauran Birai ke gudanar da al’amuransu na yau da kullum ba tare da shiga ba. dalili kuwa shi ne wadannan Birai sun yi wayo ne a kebe, ba su samu damar koyon yadda a ke mu’amala da sauran ‘yan uwa Birai ba.
Da wannan dan takaitaccen misali wanda na dora shi a bisa binciken ilmi na ke son tabbatarwa cewa shi Mutum ya fi Biri bukatuwa zuwa ga koyon mu’amalolin yau da gobe.
Al’amarin killace Yara kuwa wani abu ne mai girma, duk da ya ke babu yadda za a yi don kawai a na so a fahimci me zai iya faruwa idan an killace su, sai masana halayyar dan Adam da zamantakewa su debi Jarirai su killace su a matsayin gwaji. Amma daga bincike da a ka gudanar dangane da irin sakacin da iyaye ke yi ko kuma wadanda a ke dauka domin rainon jarirai ke yi, an tattara bayanai sosai dangane da irin hadurrra da ke cikin killace Yaro. Zan yi kokarin kawo misalan binciken da a ka gudanar wadanda a cikinsu akwai darussa da ke nuni da hadurran aikata hakan.
Akwai wata yarinya da a ka haifa a shekarar 1932 mai suna Anna, iyayenta ba aure su ka yi a ka haife ta ba, bilhasali ma mahaifiyarta na da matsalar tabin kwakwalwa, saboda haka tun kafin haihuwarta babu wanda ya damu da ta rayu ko ta mutu. A haka a ka haifi Anna, wacce cikin rashin kulawa da nunawa damuwa a ka killace ta a wani kuryan daki da ke gidan mahaifin uwarta. Mahaifiyarta ta na fita tun da asuba ta tafi gona kuma sai dare ya yi nisa ta ke dawowa. Saboda haka ne Anna ba ta samu kulawa da kauna kamar yadda sauran ‘ya ‘ya ke samu.
Masanin halayyar jama’a da zamantakewa Kingsley Dabis a shekarar 1940 ya yi fashin baki dangane da halin da a ka tsinci Anna a shekarar 1938, kamar haka: (Anna) ba ta iya yin magana kamar yadda dan Adam ke yi, haka nan kuma ba ta iya yin tafiya kamar yadda kowa ke yi, ba ta fahimta don an alamta mata abu da hannu, ba ta iya cin abinci da kanta ko da an ajiye mata abincin a gabanta, sannan ba ta san menene tsafta ko kazanta ba.
Wannan al’amari duk ya faru da Anna ne a cikin shekaru shida a killace. A dai dai wannan lokaci ne a ka sa ka ta a makaranta ta musamman, inda a hankali ta fara koyon yadda a ke tafiya da kafafu biyu, yin magana, da kuma tsaftace kanta. Anna ta na ‘yar shekaru 10 a duniya ta mutu, amma kafin mutuwarta an ruwaito cewa ta koyi yadda a ke bin umurni, yin magana, wanke hannayenta biyu, goge bakinta tare da kokarin taimakon wasu Yaran.
A shekarar 1970 an tsinci wata yarinya ‘yar shekaru 13 mai suna Genie. Ita Genie an tsince ta ne a wani kullallen daki ita kadai tun ta na ‘yar watanni 20 a duniya. Mahaifiyarta ta yi haka ne saboda ba ta son a san ta haihu. Sai ta rika watsawa yarinyar abinci ta tagar dakin. Genie ba ta taba jin sautin dan Adam ba, saboda babu wanda ya taba yi mata magana, haka kuma babu talabijin ko Rediyo a dakin.
Masanan da su ka amshi Genie bayan an tsinto ta sun bayyana ta kaamar haka: a lokacin da a ka kawo ta sam ba ta san wani abu wai shi mu’amala ba. ba ta san ya a ke yin fitsari ko bayan gari ba, ba ta iya cin abinci yadda mutane ke tattaunawa a baki kafin su hadiye ba. ba ta iya rike fitsarinta balle bayan gari. Saboda rashin tauna abincin da ta ke yi a lokacin da a ka tsince ta, girman jikinta da tsawonta bai fi na Yaro mai rabin shekarunta ba.
Da wadannan ‘yan misalai za mu iya fahimtar cewa shi killace Yaro a hana shi mu’amala da mutane babban hadari ne wanda zai jefa yaron cikin sahun wadanda ba su iya mu’amala da mutane ba. kuma wannan rashin iya mu’amala na iya ci gaba da tasiri a rayuwar mutum har zuwa girmanshi, ta yadda za ka ga mutum cikakke amma idan ya kwafso maka wani shirmen sai ka dauka dan firamare ne.
Mu hadu mako mai zuwa
Monday, 7 September 2015
Taqaddama: MUGUNTA DA MUSABBABINTA 'AGGRESSION'
A wata taqaddama mai sarqaqiya, an ce kowanne mutum ma mugu ne, an ce kowa na da nau’in mugunta a cikin jininshi, sai dai wani mugun ya gawurta fiye da wani.
Ma’anar mugunta a fannin ilmin zamantakewa da sanin halayyar jama’a shi ne cutar da mutane bisa ganganci. Dalilin da ya sa mu ka mayar da hankali wurin karantar mugunta shi ne bisa la’akari da yadda mugaye su ka yi wa duniya yawa.
Saboda qoqarin ganin an fahimci mugunta da nau’o’inta, masana a wannan fanni sun kasu kashi uku; ‘yan sahun farko su ne wadanda su ka tafi a kan cewa mugunta halitta ce wacce a ke haifo mutum da ita ko kuma a ke iya gadonta. ‘yan sahu na biyu kuma su ne wadanda ke da ra’ayin cewa babu ruwan dabi’a ko gado da muguntar mutum. A yanzu an samu kaso na uku, wadanda su kuma ke ganin mugunta ta tattara abubuwa da yawa, ba abu guda daya ba ne ke zama dalilinta.
Akwai mugunta wacce ta qumshi cutar da gangar jikin mutum – misali mangari, naushi, caccaka wuqa, ko kuma harbi da bindiga ko kibiya. daya sashen mugunta shi ne wanda bai qumshi cutarwa kaitsaye ga gangan jikin mutum ba. Irin wannan muguntar sun hada da ta fatar baki, irinsu yiwa mutum ihu, rantsuwa bisa shaidar zir. Cikin irin wannan muguntar har da yin gulma domin cin zarafin wani mutum. akwai kuma wata samfurin mugunta wacce ba ta buqatar magana da fatar baki, kawai sai dai a yi amfani da alami, misali fashewa da dariya yayin da wani ya shigo wuri. Toshe hanci a yayin da wani ya gifta, da dai sauransu.
Zan bibiyi wadannan mabambantan ra’ayi ta yadda hatta mai karatu zai iya fahimtar daga ina mugayen da ke zagaye da shi su ka samo muguntarsu. Idan kuma kai ne mugun, bayan karanta musabbabin mugunta za ka so ka yi qoqarin daqile ta ko rage tasirinta a kanka.
Wadanda su ka ce mugunta a na haihuwar mutane ne da ita sun tafi a kan cewa akwai wata qwayar halitta mai suna ‘Thenatos’ wacce a ke haihuwar kowanne dan Adam da ita. Ita wancan qwayar halitta ne ke ingiza mutane wurin aiwatar da duk wani nau’in mugunta a kan mutane.
A wurin masu irin wancan fahimtar sun ce ita qwayar halittar ‘Thenatos’ an halicci mutum ne da ita a matsayin wani sindari da zai rusa shi. A maimakon mutum ya bari wannan qwayar halitta ta ‘Thenatos’ ta rusa shi, sai a riqa yin amfani da ita wurin cutar da mutane, dabbobi ko wasu halittun da ke kusa da shi.
Masanan sun ci gaba da cewa, idan a cikin mutane ka ga wani mutum wanda bai fiye aikata mugunta ba; ire iren wadannan mutanen su na danne waccan qwayar halittan ne ta yadda sai dai ta ci gaba da cutar da su.
Babban misali a nan shi ne, mutumin da ya qware a mugunta ba ya buqatar sai an tsokane shi ko an aikata wani aiki sannan zai aikata muguntan. Zai iya daukan mota ya hau titi ya na mugun gudun da zai riqa tsoratar da mutane, wasu lokutan ma har ya hau ta kan wasu. Ka ga kenan wannan mugun bai buqatar wani dalili kafin ya aikata. Amma akwai a cikin mutane wadanda ko ka nemi rikicinsu, za su danne su bar komi ya wuce. Za ka ga wani, an zo da mota an yi mishi tuqin ganganci har ma a yi mishi barna, amma wannan ba zai sa shi ma ya mayar da ganganci ba balle ya aikata barna.
bangaren wadanda ke ganin babu wata alaqa tsakanin mugunta da qwayar halitta sun bayyana ne sakamakon martani da raddi da su ka dabaibaye wancan ra’ayin na farko. Su kuma wadannan sun tafi ne a kan cewa mutum na zama mugu ne sakamakon tursasawa. Ma’anan tursasawa a nan shi ne a kange mutum daga cimma wani muradi na shi ko kuma a tauye mishi wani haqqi da ya ke ganin na shi ne.
Masu wannan ra’ayin na alaqanta mugunta da tursasawa sun tafi a kan cewa yanayin yadda za ka tursasa mutum yanayin irin samfurin muguntan da zai aikata maka. Shi ya sa a wurinsu mugunta ta fi yawa a wurin wadanda ba su da aikin yi, da wurin wadanda ba su da kudi, da kuma wurin wadanda su ka sha kaye a fagen soyayya.
Misali a nan shi ne, idan har a ka samu yawan matasa wadanda ba su da aikin yi a gari, wannan rashin aikin yi shi ne zai tursasa matasan su riqa sa kansu a cikin rikice rikicen da za su iya kaiwa ga salwantar rayuka, qone qone da sace sace.
Haka kuma idan mutum biyu su na neman budurwa daya. Sai na farko ya samu dacen sace zuciyar yarinyar, har ta kai idan na biyun ya zo zance, sai na farkon (wanda ya sace zuciyarta) ya zo ya janye ta gefe, sannan kuma su yi ta sheqewa da dariya; wannan irin cin fuska da su ke yi mai zai tursasa shi ya aiwatar da kowanne irin nau’in mugunta a kansu.
Shi ma wannan nazarin na alaqanta mugunta da tursasawa ya sha raddi da martani; martanin ne ma ya samar da wani nazarin dangane da mugunta, wanda ya tafi a kan cewa babu wani abu qwaya daya tak da ke zama musabbabin mugunta. A wannan fahimtar, mugunta babu ruwanta da qwayar halitta, sannan babu ruwanta da tursasawa. Ita mugunta a na koyonta ne kamar yadda a ke koyon sauran dabi’u. ta hanyoyin da a ke bi a koyi sauran dabi’u ta su kuma a ke bi a koyi mugunta.
Idan mutum ya fiye kallon fima fiman mugunta, babu makawa zai fara gina dabi’ar mugunta. Wanda a kodayaushe bai da aiki sai kallon fima fiman da Amurkawa ke yi, a na kwano da mota a na rusa gidaje da qaddamar da mugunta iri iri, akwai yiwuwar duk ranar da wannan mutumi ya dauki mota ya yi qoqarin gwada abin da ya ke kallo.
Kamar yadda mu ke koyon mu gaisa da mutane, haka nan mu ke koyon mu mari mutane. Kamar yadda mu ke koyon mu yi wa mutum murmushi haka nan mu ke koyon mu zare wa mutum ido don ya ji tsoro. Saboda haka idan a ka ce wai tursasawa ne ke janyo mugunta, sai mu ce ai akwai mutanen da mu ka sani wadanda za a tursasa su a kai su bango amma su hadiye fushinsu. Haka kuma yadda a ke samun mugaye a cikin talakawa haka nan a ke samu a tsakanin masu dukiya. Mugunta ba komi bace face wata dabi’a wacce mu ke koyo a muhallin da mu ke rayuwa; idan mu ka tsinci kawunanmu a tsakiyar mugaye, za mu ginu da dabi’ar yi wa mugunta kallon abu me kyau. Mu hadu mako mai zuwa!
Ma’anar mugunta a fannin ilmin zamantakewa da sanin halayyar jama’a shi ne cutar da mutane bisa ganganci. Dalilin da ya sa mu ka mayar da hankali wurin karantar mugunta shi ne bisa la’akari da yadda mugaye su ka yi wa duniya yawa.
Saboda qoqarin ganin an fahimci mugunta da nau’o’inta, masana a wannan fanni sun kasu kashi uku; ‘yan sahun farko su ne wadanda su ka tafi a kan cewa mugunta halitta ce wacce a ke haifo mutum da ita ko kuma a ke iya gadonta. ‘yan sahu na biyu kuma su ne wadanda ke da ra’ayin cewa babu ruwan dabi’a ko gado da muguntar mutum. A yanzu an samu kaso na uku, wadanda su kuma ke ganin mugunta ta tattara abubuwa da yawa, ba abu guda daya ba ne ke zama dalilinta.
Akwai mugunta wacce ta qumshi cutar da gangar jikin mutum – misali mangari, naushi, caccaka wuqa, ko kuma harbi da bindiga ko kibiya. daya sashen mugunta shi ne wanda bai qumshi cutarwa kaitsaye ga gangan jikin mutum ba. Irin wannan muguntar sun hada da ta fatar baki, irinsu yiwa mutum ihu, rantsuwa bisa shaidar zir. Cikin irin wannan muguntar har da yin gulma domin cin zarafin wani mutum. akwai kuma wata samfurin mugunta wacce ba ta buqatar magana da fatar baki, kawai sai dai a yi amfani da alami, misali fashewa da dariya yayin da wani ya shigo wuri. Toshe hanci a yayin da wani ya gifta, da dai sauransu.
Zan bibiyi wadannan mabambantan ra’ayi ta yadda hatta mai karatu zai iya fahimtar daga ina mugayen da ke zagaye da shi su ka samo muguntarsu. Idan kuma kai ne mugun, bayan karanta musabbabin mugunta za ka so ka yi qoqarin daqile ta ko rage tasirinta a kanka.
Wadanda su ka ce mugunta a na haihuwar mutane ne da ita sun tafi a kan cewa akwai wata qwayar halitta mai suna ‘Thenatos’ wacce a ke haihuwar kowanne dan Adam da ita. Ita wancan qwayar halitta ne ke ingiza mutane wurin aiwatar da duk wani nau’in mugunta a kan mutane.
A wurin masu irin wancan fahimtar sun ce ita qwayar halittar ‘Thenatos’ an halicci mutum ne da ita a matsayin wani sindari da zai rusa shi. A maimakon mutum ya bari wannan qwayar halitta ta ‘Thenatos’ ta rusa shi, sai a riqa yin amfani da ita wurin cutar da mutane, dabbobi ko wasu halittun da ke kusa da shi.
Masanan sun ci gaba da cewa, idan a cikin mutane ka ga wani mutum wanda bai fiye aikata mugunta ba; ire iren wadannan mutanen su na danne waccan qwayar halittan ne ta yadda sai dai ta ci gaba da cutar da su.
Babban misali a nan shi ne, mutumin da ya qware a mugunta ba ya buqatar sai an tsokane shi ko an aikata wani aiki sannan zai aikata muguntan. Zai iya daukan mota ya hau titi ya na mugun gudun da zai riqa tsoratar da mutane, wasu lokutan ma har ya hau ta kan wasu. Ka ga kenan wannan mugun bai buqatar wani dalili kafin ya aikata. Amma akwai a cikin mutane wadanda ko ka nemi rikicinsu, za su danne su bar komi ya wuce. Za ka ga wani, an zo da mota an yi mishi tuqin ganganci har ma a yi mishi barna, amma wannan ba zai sa shi ma ya mayar da ganganci ba balle ya aikata barna.
bangaren wadanda ke ganin babu wata alaqa tsakanin mugunta da qwayar halitta sun bayyana ne sakamakon martani da raddi da su ka dabaibaye wancan ra’ayin na farko. Su kuma wadannan sun tafi ne a kan cewa mutum na zama mugu ne sakamakon tursasawa. Ma’anan tursasawa a nan shi ne a kange mutum daga cimma wani muradi na shi ko kuma a tauye mishi wani haqqi da ya ke ganin na shi ne.
Masu wannan ra’ayin na alaqanta mugunta da tursasawa sun tafi a kan cewa yanayin yadda za ka tursasa mutum yanayin irin samfurin muguntan da zai aikata maka. Shi ya sa a wurinsu mugunta ta fi yawa a wurin wadanda ba su da aikin yi, da wurin wadanda ba su da kudi, da kuma wurin wadanda su ka sha kaye a fagen soyayya.
Misali a nan shi ne, idan har a ka samu yawan matasa wadanda ba su da aikin yi a gari, wannan rashin aikin yi shi ne zai tursasa matasan su riqa sa kansu a cikin rikice rikicen da za su iya kaiwa ga salwantar rayuka, qone qone da sace sace.
Haka kuma idan mutum biyu su na neman budurwa daya. Sai na farko ya samu dacen sace zuciyar yarinyar, har ta kai idan na biyun ya zo zance, sai na farkon (wanda ya sace zuciyarta) ya zo ya janye ta gefe, sannan kuma su yi ta sheqewa da dariya; wannan irin cin fuska da su ke yi mai zai tursasa shi ya aiwatar da kowanne irin nau’in mugunta a kansu.
Shi ma wannan nazarin na alaqanta mugunta da tursasawa ya sha raddi da martani; martanin ne ma ya samar da wani nazarin dangane da mugunta, wanda ya tafi a kan cewa babu wani abu qwaya daya tak da ke zama musabbabin mugunta. A wannan fahimtar, mugunta babu ruwanta da qwayar halitta, sannan babu ruwanta da tursasawa. Ita mugunta a na koyonta ne kamar yadda a ke koyon sauran dabi’u. ta hanyoyin da a ke bi a koyi sauran dabi’u ta su kuma a ke bi a koyi mugunta.
Idan mutum ya fiye kallon fima fiman mugunta, babu makawa zai fara gina dabi’ar mugunta. Wanda a kodayaushe bai da aiki sai kallon fima fiman da Amurkawa ke yi, a na kwano da mota a na rusa gidaje da qaddamar da mugunta iri iri, akwai yiwuwar duk ranar da wannan mutumi ya dauki mota ya yi qoqarin gwada abin da ya ke kallo.
Kamar yadda mu ke koyon mu gaisa da mutane, haka nan mu ke koyon mu mari mutane. Kamar yadda mu ke koyon mu yi wa mutum murmushi haka nan mu ke koyon mu zare wa mutum ido don ya ji tsoro. Saboda haka idan a ka ce wai tursasawa ne ke janyo mugunta, sai mu ce ai akwai mutanen da mu ka sani wadanda za a tursasa su a kai su bango amma su hadiye fushinsu. Haka kuma yadda a ke samun mugaye a cikin talakawa haka nan a ke samu a tsakanin masu dukiya. Mugunta ba komi bace face wata dabi’a wacce mu ke koyo a muhallin da mu ke rayuwa; idan mu ka tsinci kawunanmu a tsakiyar mugaye, za mu ginu da dabi’ar yi wa mugunta kallon abu me kyau. Mu hadu mako mai zuwa!
Mu Fahimci Dabi’ar MUTUM 'ATTITUDE'
Matsalolin da ke tattare da yawancin ma’aikatu, masana’antu, cibiyoyi da hukumomi ba komi ba ne face matsalar rashin sanin dabi’un dan Adam. dabi’a aba ce me wahalan sha’ani, kadan ne daga cikin mutane su ke yin mu’amala da mutum a lokaci guda kuma su ke karantar dabi’arsa. Sau da yawa kawai mu’amala da fankon mutum mu ke yi, ba tare da nazarin dabi’arsa dangane da abubuwa ba.
dabi’ar mutum ne ke taimakonsa ya fassara yanayi, kuma duk ta yadda ya yi fassaran yanayi a haka zai tafiyar da shi, kuma da wannan fassarar ne zai duba ya gani shin wacce irin mu’amala zai yi a dai dai lokacin.
dabi’un mutane sun bambanta, sai dai a wasu lokutan a kan samu wani babban al’amari wanda ke zama sanadin haifarwa da mutane dabi’a iri guda. Misali a nan shi ne, a shekarar 2003 lokacin da qasar Amurka ta shirya za ta yaqi qasar Iraqi, mutanen qasar Amurka sun yi ta zanga zangan Allah wadai da wannan yaqi da a ke son gabatarwa. Wannan ya nuna mana cewa, mutanen Amurka sun gaji da yaqe yaqen da qasar ke shiga, saboda haka yawan yaqin da qasarsu ke yi sai ya haifar musu da dabi’ar qin jinin yaqi.
Akwai wasu abubuwa da dabi’ar mutum ne kadai ke kai shi ga aikata su. Na farko, dabia ce kadai ke sa mu qaunaci mutum ko mu qi shi, ita ke sa mu ji mu na son wasu gungun mutane ko qungiya. Haka nan dabi’arka ce kadai za ta iya zartarwa ka danganta kanka da qungiya; kamar misali idan dabi’arka ba ta qaunar tsiraici da kallon batsa, babu yadda za a yi ka kasance ma’abocin kallon fima fiman da ‘yan Kudancin Nijeriya ke yi a yanzu ‘Nigerian Films’, saboda dabi’arka ba ta son kallon irinsu, ko da bisa kuskure ka zo inda a ke kallo, yanayin fuskarka da yadda ka ke yi, zai nuna cewa ka ginu da dabi’ar qin irin wannan fima fimai.
Na biyu shi ne, da dabi’a mutum ke dubawa ya ga shin idan ya aikata wani aiki me zai biyo baya? A nan za mu iya cewa saboda son biyan buqatar mutum ya na iya aikata dabi’un da zasu kai shi ga cimma muradunsa . Misali, mutumin da ya hango diyar wani ya na so, zai yi qoqarin ko ta wanne hali ya riqa aikata dabi’u masu kyau a wuraren da ya ke tsammanin mahaifin yarinyar ko wasu makusantanshi. Ba kawai biyan buqatun mutum ba, da dabi’a mutum ke kiyaye abubuwan da za su iya kasancewa barazana gare shi. Misali a nan shi ne, bayan da a ka samu sabuwar gwamnati a Nijeriya; da yawan manyan mutane sun fara sassauta dabi’unsu na almubazaranci, da almundahana saboda gudun kar Shugaban qasa Buhari ya yi sukuwa a kansu. Wannan dabi’ar ta ginu ne saboda tsoro.
Na uku, a sau da yawa za ka ga wasu mutane na aikata abu babu kyawun gani. Su a wurinsu dabi’arsu ce ke nuna musu cewa wannan abu da su ke aikatawa dai dai ne. Abu daya ne ke dai daita dabi’ar mutum zuwa mai kyau kuma ta-gari, shi ne ilmi. Ilmi na da muhimmancin gaske wurin tasiri ga dabi’ar mutum. Misali a nan shi ne, za ka ga mutumin da bai je makarantar jami’a ba ko gaba da sakandare, zai tashi da wata irin dabi’a ta gani – gani ga duk wata qabila da ba ta shi ba. Amma a lokacin da mutum ya samu damar halartar makarantun gaba da jami’a, inda kusan kowacce qabila ta na da ‘ya ‘yanta a matsayin dalibai, bayan dogon lokacin da mutum zai dauka ya na karatu tare da mu’amala da mutane daga qabilu daban daban, za ka ga ya samu chanji a dabi’arsa daga qin jini ko gani – gani ga wasu qabilun da ba nashi ba.
Na hudu, dabi’ar mutum ne ke ba shi dama ya bayyanawa duniya ko shi wanene, dabi’arsa ce ke ba shi daman bayyana al’adarshi da irin halayenshi. Kamar misali, a shekarun baya da su ka shude a jihar Kano, idan ka ga mutum da jar hula, babu tantama wannan jar hula na alamta qauna ne ko shauqin Malam Aminu Kano. A yanzu kuma idan ka ga mutum da hula a Kano, mutane na saurin fassara shi ne da kasancewa dan Kwankwasiyya. Wannan ne ya sa da yawan dattawa (tsofaffi) a cikin garin Kano su ka watsar da jajayen hulunansu (Na Malam Aminu Kano) saboda su ba’yan kwankwasiyya ba ne, kuma ba su so a fassara su a haka.
Duk da dabi’a ba wata aba ba ce da a ke iya gani da ido, ko a taba, amma a na iya auna ta. Wannan ba sabon abu ba ne. idan ka na so ka fahimci inda dabi’ar mutum ta dosa dangane da wani al’amari bari ka ji yadda a ke auna dabi’a. Akwai wasu hanyoyin auna dabi’a da yawan gaske wadanda mu ke amfani da su, amma mafi sauqin ciki zan yi bayani a kai.
Kamar misali, ka na so ka fahimci shin menene ra’ayin mutum dangane da auren zawarawa da wasu gwamnoni ke bayarwa. Sai ka yi mishi tambaya kamar haka; Shin ka na goyon bayan auren zawaran da gwamnati ke jagoranta? Kai za ka qayyade amsoshin da mai amsawa zai zaba, ba wai za ka barshi ya yi ta zubo bayani ba ne. misali sai ka bashi zabi biyu; Eh ko A’a.
Duk amsar da wanda a ka tambaya ya zaba a cikin biyun, da su za ka auna dabi’arsa dangane da auren zawarawa. Idan ya zabi EH. Shi kenan ka gano cewa dabi’arsa dangane da auren zawarawa ta goyon baya ce, wannan zai sa ba za ka riqa fargabar yin maganan auren zawarawa da shi ba, musamman muhimmancinshi da kuma amfaninshi. Idan kuma ya zabi A’A, ya na nuna dabi’arsa ba ta qaunar auren zawarawan da a ke yi, shi zai sa ka kiyaye yawan matsawa a kan auren zawarawa a duk wata tattaunawarka ko mu’amalarka da wannan mutumin. Mu hadu mako mai zuwa
dabi’ar mutum ne ke taimakonsa ya fassara yanayi, kuma duk ta yadda ya yi fassaran yanayi a haka zai tafiyar da shi, kuma da wannan fassarar ne zai duba ya gani shin wacce irin mu’amala zai yi a dai dai lokacin.
dabi’un mutane sun bambanta, sai dai a wasu lokutan a kan samu wani babban al’amari wanda ke zama sanadin haifarwa da mutane dabi’a iri guda. Misali a nan shi ne, a shekarar 2003 lokacin da qasar Amurka ta shirya za ta yaqi qasar Iraqi, mutanen qasar Amurka sun yi ta zanga zangan Allah wadai da wannan yaqi da a ke son gabatarwa. Wannan ya nuna mana cewa, mutanen Amurka sun gaji da yaqe yaqen da qasar ke shiga, saboda haka yawan yaqin da qasarsu ke yi sai ya haifar musu da dabi’ar qin jinin yaqi.
Akwai wasu abubuwa da dabi’ar mutum ne kadai ke kai shi ga aikata su. Na farko, dabia ce kadai ke sa mu qaunaci mutum ko mu qi shi, ita ke sa mu ji mu na son wasu gungun mutane ko qungiya. Haka nan dabi’arka ce kadai za ta iya zartarwa ka danganta kanka da qungiya; kamar misali idan dabi’arka ba ta qaunar tsiraici da kallon batsa, babu yadda za a yi ka kasance ma’abocin kallon fima fiman da ‘yan Kudancin Nijeriya ke yi a yanzu ‘Nigerian Films’, saboda dabi’arka ba ta son kallon irinsu, ko da bisa kuskure ka zo inda a ke kallo, yanayin fuskarka da yadda ka ke yi, zai nuna cewa ka ginu da dabi’ar qin irin wannan fima fimai.
Na biyu shi ne, da dabi’a mutum ke dubawa ya ga shin idan ya aikata wani aiki me zai biyo baya? A nan za mu iya cewa saboda son biyan buqatar mutum ya na iya aikata dabi’un da zasu kai shi ga cimma muradunsa . Misali, mutumin da ya hango diyar wani ya na so, zai yi qoqarin ko ta wanne hali ya riqa aikata dabi’u masu kyau a wuraren da ya ke tsammanin mahaifin yarinyar ko wasu makusantanshi. Ba kawai biyan buqatun mutum ba, da dabi’a mutum ke kiyaye abubuwan da za su iya kasancewa barazana gare shi. Misali a nan shi ne, bayan da a ka samu sabuwar gwamnati a Nijeriya; da yawan manyan mutane sun fara sassauta dabi’unsu na almubazaranci, da almundahana saboda gudun kar Shugaban qasa Buhari ya yi sukuwa a kansu. Wannan dabi’ar ta ginu ne saboda tsoro.
Na uku, a sau da yawa za ka ga wasu mutane na aikata abu babu kyawun gani. Su a wurinsu dabi’arsu ce ke nuna musu cewa wannan abu da su ke aikatawa dai dai ne. Abu daya ne ke dai daita dabi’ar mutum zuwa mai kyau kuma ta-gari, shi ne ilmi. Ilmi na da muhimmancin gaske wurin tasiri ga dabi’ar mutum. Misali a nan shi ne, za ka ga mutumin da bai je makarantar jami’a ba ko gaba da sakandare, zai tashi da wata irin dabi’a ta gani – gani ga duk wata qabila da ba ta shi ba. Amma a lokacin da mutum ya samu damar halartar makarantun gaba da jami’a, inda kusan kowacce qabila ta na da ‘ya ‘yanta a matsayin dalibai, bayan dogon lokacin da mutum zai dauka ya na karatu tare da mu’amala da mutane daga qabilu daban daban, za ka ga ya samu chanji a dabi’arsa daga qin jini ko gani – gani ga wasu qabilun da ba nashi ba.
Na hudu, dabi’ar mutum ne ke ba shi dama ya bayyanawa duniya ko shi wanene, dabi’arsa ce ke ba shi daman bayyana al’adarshi da irin halayenshi. Kamar misali, a shekarun baya da su ka shude a jihar Kano, idan ka ga mutum da jar hula, babu tantama wannan jar hula na alamta qauna ne ko shauqin Malam Aminu Kano. A yanzu kuma idan ka ga mutum da hula a Kano, mutane na saurin fassara shi ne da kasancewa dan Kwankwasiyya. Wannan ne ya sa da yawan dattawa (tsofaffi) a cikin garin Kano su ka watsar da jajayen hulunansu (Na Malam Aminu Kano) saboda su ba’yan kwankwasiyya ba ne, kuma ba su so a fassara su a haka.
Duk da dabi’a ba wata aba ba ce da a ke iya gani da ido, ko a taba, amma a na iya auna ta. Wannan ba sabon abu ba ne. idan ka na so ka fahimci inda dabi’ar mutum ta dosa dangane da wani al’amari bari ka ji yadda a ke auna dabi’a. Akwai wasu hanyoyin auna dabi’a da yawan gaske wadanda mu ke amfani da su, amma mafi sauqin ciki zan yi bayani a kai.
Kamar misali, ka na so ka fahimci shin menene ra’ayin mutum dangane da auren zawarawa da wasu gwamnoni ke bayarwa. Sai ka yi mishi tambaya kamar haka; Shin ka na goyon bayan auren zawaran da gwamnati ke jagoranta? Kai za ka qayyade amsoshin da mai amsawa zai zaba, ba wai za ka barshi ya yi ta zubo bayani ba ne. misali sai ka bashi zabi biyu; Eh ko A’a.
Duk amsar da wanda a ka tambaya ya zaba a cikin biyun, da su za ka auna dabi’arsa dangane da auren zawarawa. Idan ya zabi EH. Shi kenan ka gano cewa dabi’arsa dangane da auren zawarawa ta goyon baya ce, wannan zai sa ba za ka riqa fargabar yin maganan auren zawarawa da shi ba, musamman muhimmancinshi da kuma amfaninshi. Idan kuma ya zabi A’A, ya na nuna dabi’arsa ba ta qaunar auren zawarawan da a ke yi, shi zai sa ka kiyaye yawan matsawa a kan auren zawarawa a duk wata tattaunawarka ko mu’amalarka da wannan mutumin. Mu hadu mako mai zuwa
SAUYI A CIKIN AL’UMMA: NAZARIN BUKIN ZAGAYOWAR RANAR HAIHUWA (Birthday)
Kowanne mutum a duniya haifo shi a ka yi, babu wani tarihi da ya riske mu a kan cewa ga wani wanda shi fadowa ya yi daga sama, ba a jariri ba, da girmanshi da wayonshi. Wannan dalili na cewa kowanne mutum haihuwarsa a ka yi a duniya ne ya samar da ranar haihuwa.
A tsohuwar al’adar Malam Bahaushe, a ranar da a ka haifi mutum ba dole ba ne sai ya zama iyayenshi sun kiyaye kwanan wata da shekara, sai dai a kan yi wani abu mai ban sha’awa shi ne yi wa mutum lakabi da sunan ranar da a ka haife shi.
Wadanda a ka haifa a ranar Juma’a, a kan kirasu da Danjuma ko Danjummai, mace kuma a kira ta da Jummai ko Juma. Macen da a ka haifa ranar Laraba kuwa sunanta Balaraba, shi namijin Balarabe ko kuma Bala. Ranar litinin shi ne Dan liti, ranar Talata kuma dan tala.
Nazarin wadannan sunaye su ma abubuwa ne masu tasiri wanda su na da muhallinsu a ilmin sanin halayyar Jama’a.
Sauyi a cikin al’umma wani al’amari ne da ya zama wajibi, ba a iya kaucewa sauyi. Ko a na so ko ba a so ya na afkuwa. Kuma wani abun ban sha’awa da sauyi shi ne duk inda mutum ya je a fadin duniyar nan zai shaidi sauyin.
Haka kuma sauyi kan dauki salon faruwa a cikin karamin lokaci ko kuma lokaci mai tsawo. Wani al’ada na sauyi shi ne idan a ka samu sauyi a wani bangare na al’umma yak an shafi sauran bangarori.
Misali idan a ka samu sauyi a yanayin auratayya tsakanin mutane, wannan sauyi na iya shafar al’ada, idan sauyin da ya afku a yanayin auratayya ya afku ne ta fuskacin samuwar aure tsakanin kabilu mabambanta ba tare da la’akari da bambanci ba. Za a samu sauyi ne ta yanayin cakuduwar al’adu.
Wani sauyin mutane ne ke tsara shi yadda zai auku, wani kuma ya na aukuwa ne ba tare da sanin mutane ba. Misali, mutane kan sauya yanayin shigarsu (sanya tufafi) a lokacin da yanayin sanyi ya kankama. Sanyin ke takura mutum ya yi shigan da bai saba da it aba. A wuraren da dusar kankara ke sauka, sai ka ga wannan dusar ta tilasta musu yin wani irin shiga, wanda babu yadda wani a yankin da babu dusar ya yi irinta.
Cikin sauye sauyen da a ka samu a Nijeriya, mafi tasiri shi ne tasirin al’adar Bature a kasashen da ya mamaye a Afrika. Kamar a Nijeriya, an samu sauye sauye a yanayin zamantakewa; auratayya, buki, aiki (sana’o’i), tsarin abinci, sutura da sauransu.
Cikin kuskuren da Bature ya tafka a kasashen Afrika shi ne karfa karfan da ya yiwa kakanninmu wurin raba su da al’adunsu, ta hanyar shigo musu da nashi, tare da nuna musu al’adunshi a matsayin mafiya fifiko da dacewa ga rayuwar mutum.
Su ka fara sanyawa mutane dokokin tara iyali, kayyade haihuwa da auren mace guda daya rak, wai duk a sunan kiyaye bunkasar tattalin arzikin kasa. duk wannan bai kawar da mutanenmu 100% bisa 100% daga al’adunsu ba.
Amma zuwan zamani, musamman bayyanar al’amarin ‘Globalisation’ dunkulewar duniya wuri guda ya haifar da sauye sauye a al’ummu fiye da tsammani. A yanzu abun da ke faruwa a birnin Ingila, wanda ke zaune a kauyen Neja zai iya kallo kaitsaye, ko dai ta wayar salula ko ta yanar gizo a na’urar kwamfuta ko tashar talabijin.
Wannan ilmin sanin me ke faruwa a sassa daban daban na duniya ya taimaka wurin samun sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa. Ta yadda an jima a na kiyaye wacce rana a ka haifi mutum, wanne wata, a wacce shekara.
Don haka idan shekara ta zagayo, dai dai wannan ranar a cikin watan da a ka haifi mutum, akwai buki na musamman da a ke shiryawa na tunawa da wannan rana ta haihuwa, wasu yaran ma iyayensu ke shirya musu, har zuwa su girma su shiryawa kawunansu.
Al’adar bukin zagayowar ranar haihuwa, ba a kowacce al’ada ba ne akwai shi. Amma yanzu kuma ya zama a bu mafi wahalan gaske a rasa shi a cikin al’umma, komi kankanta akwai.
Ya zuwa yanzu ma sauyi ya sake bayyana a yanayin wannan murna na zagayowar ranar haihuwa a Nijeriya. Yadda masu dukiya ke wannan murnar ta bambanta da yadda talakawa ke yi, duk da ya ke talakawan na ta kokarin ko ta halin kaka sai sun kwaikwayi masu kudi, su kuma masu kudin hankoronsu sai sun kwaikwayi turawa.
A farko farkon bayyanar guguwar sauyin bukin zagayowar ranar haihuwa, yadda a ke taron shi ne a yi alkaki ‘cake’, ‘yan uwa da abokan arziki su taru, a yanka a ci, sannan a yi buki, masu bayar da kyauta ‘gift’ su bayar.
Wannan al’ada ce ta masu kudi, musamman a Nijeriya, idan su na aikata wani aiki talaka ya fara kwaikwayo, sai su yi kokarin yin kari ko sauya na su don a ga bambanci. Tunda talakawa ma na rufe ido su kwaikwaiyi yanka ‘cake’, sai kuma a ka samu sauyin fara yin babban buki, wanda za a ce ga kalan kayan da a ke so mahalarta su sanya, (misali, bakin wando da jar riga), sannan kuma a kama hayan wani babban otal wanda a can za a yi bukin.
Wannan sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa ya sa mata da yawa a yanzu na yin karyar ranar haihuwarsu, wata ma saboda kyaututtukan da samari kan kawo mata, ta kan shirya bukin zagayowar ranar haihuwa sau uku a shekara daya.
Mafi muhimmanci a yanzu ba wai kiyaye ranar haihuwar ba ne ma kawai, a’a bukin da ke cikin ranar a ke yi mawa, kyautar da za a samu a ke yi mawa, wanda a irin kyaututtukan wata har sabuwar mota fil a ke bata, wata kuma kudade. bukin dai ya zama jari. Toh ku taya ni murna da addu’a, nawa na gaske ne, ni ma ranar haihuwata ta zagayo. Mu hadu mako mai zuwa!
A tsohuwar al’adar Malam Bahaushe, a ranar da a ka haifi mutum ba dole ba ne sai ya zama iyayenshi sun kiyaye kwanan wata da shekara, sai dai a kan yi wani abu mai ban sha’awa shi ne yi wa mutum lakabi da sunan ranar da a ka haife shi.
Wadanda a ka haifa a ranar Juma’a, a kan kirasu da Danjuma ko Danjummai, mace kuma a kira ta da Jummai ko Juma. Macen da a ka haifa ranar Laraba kuwa sunanta Balaraba, shi namijin Balarabe ko kuma Bala. Ranar litinin shi ne Dan liti, ranar Talata kuma dan tala.
Nazarin wadannan sunaye su ma abubuwa ne masu tasiri wanda su na da muhallinsu a ilmin sanin halayyar Jama’a.
Sauyi a cikin al’umma wani al’amari ne da ya zama wajibi, ba a iya kaucewa sauyi. Ko a na so ko ba a so ya na afkuwa. Kuma wani abun ban sha’awa da sauyi shi ne duk inda mutum ya je a fadin duniyar nan zai shaidi sauyin.
Haka kuma sauyi kan dauki salon faruwa a cikin karamin lokaci ko kuma lokaci mai tsawo. Wani al’ada na sauyi shi ne idan a ka samu sauyi a wani bangare na al’umma yak an shafi sauran bangarori.
Misali idan a ka samu sauyi a yanayin auratayya tsakanin mutane, wannan sauyi na iya shafar al’ada, idan sauyin da ya afku a yanayin auratayya ya afku ne ta fuskacin samuwar aure tsakanin kabilu mabambanta ba tare da la’akari da bambanci ba. Za a samu sauyi ne ta yanayin cakuduwar al’adu.
Wani sauyin mutane ne ke tsara shi yadda zai auku, wani kuma ya na aukuwa ne ba tare da sanin mutane ba. Misali, mutane kan sauya yanayin shigarsu (sanya tufafi) a lokacin da yanayin sanyi ya kankama. Sanyin ke takura mutum ya yi shigan da bai saba da it aba. A wuraren da dusar kankara ke sauka, sai ka ga wannan dusar ta tilasta musu yin wani irin shiga, wanda babu yadda wani a yankin da babu dusar ya yi irinta.
Cikin sauye sauyen da a ka samu a Nijeriya, mafi tasiri shi ne tasirin al’adar Bature a kasashen da ya mamaye a Afrika. Kamar a Nijeriya, an samu sauye sauye a yanayin zamantakewa; auratayya, buki, aiki (sana’o’i), tsarin abinci, sutura da sauransu.
Cikin kuskuren da Bature ya tafka a kasashen Afrika shi ne karfa karfan da ya yiwa kakanninmu wurin raba su da al’adunsu, ta hanyar shigo musu da nashi, tare da nuna musu al’adunshi a matsayin mafiya fifiko da dacewa ga rayuwar mutum.
Su ka fara sanyawa mutane dokokin tara iyali, kayyade haihuwa da auren mace guda daya rak, wai duk a sunan kiyaye bunkasar tattalin arzikin kasa. duk wannan bai kawar da mutanenmu 100% bisa 100% daga al’adunsu ba.
Amma zuwan zamani, musamman bayyanar al’amarin ‘Globalisation’ dunkulewar duniya wuri guda ya haifar da sauye sauye a al’ummu fiye da tsammani. A yanzu abun da ke faruwa a birnin Ingila, wanda ke zaune a kauyen Neja zai iya kallo kaitsaye, ko dai ta wayar salula ko ta yanar gizo a na’urar kwamfuta ko tashar talabijin.
Wannan ilmin sanin me ke faruwa a sassa daban daban na duniya ya taimaka wurin samun sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa. Ta yadda an jima a na kiyaye wacce rana a ka haifi mutum, wanne wata, a wacce shekara.
Don haka idan shekara ta zagayo, dai dai wannan ranar a cikin watan da a ka haifi mutum, akwai buki na musamman da a ke shiryawa na tunawa da wannan rana ta haihuwa, wasu yaran ma iyayensu ke shirya musu, har zuwa su girma su shiryawa kawunansu.
Al’adar bukin zagayowar ranar haihuwa, ba a kowacce al’ada ba ne akwai shi. Amma yanzu kuma ya zama a bu mafi wahalan gaske a rasa shi a cikin al’umma, komi kankanta akwai.
Ya zuwa yanzu ma sauyi ya sake bayyana a yanayin wannan murna na zagayowar ranar haihuwa a Nijeriya. Yadda masu dukiya ke wannan murnar ta bambanta da yadda talakawa ke yi, duk da ya ke talakawan na ta kokarin ko ta halin kaka sai sun kwaikwayi masu kudi, su kuma masu kudin hankoronsu sai sun kwaikwayi turawa.
A farko farkon bayyanar guguwar sauyin bukin zagayowar ranar haihuwa, yadda a ke taron shi ne a yi alkaki ‘cake’, ‘yan uwa da abokan arziki su taru, a yanka a ci, sannan a yi buki, masu bayar da kyauta ‘gift’ su bayar.
Wannan al’ada ce ta masu kudi, musamman a Nijeriya, idan su na aikata wani aiki talaka ya fara kwaikwayo, sai su yi kokarin yin kari ko sauya na su don a ga bambanci. Tunda talakawa ma na rufe ido su kwaikwaiyi yanka ‘cake’, sai kuma a ka samu sauyin fara yin babban buki, wanda za a ce ga kalan kayan da a ke so mahalarta su sanya, (misali, bakin wando da jar riga), sannan kuma a kama hayan wani babban otal wanda a can za a yi bukin.
Wannan sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa ya sa mata da yawa a yanzu na yin karyar ranar haihuwarsu, wata ma saboda kyaututtukan da samari kan kawo mata, ta kan shirya bukin zagayowar ranar haihuwa sau uku a shekara daya.
Mafi muhimmanci a yanzu ba wai kiyaye ranar haihuwar ba ne ma kawai, a’a bukin da ke cikin ranar a ke yi mawa, kyautar da za a samu a ke yi mawa, wanda a irin kyaututtukan wata har sabuwar mota fil a ke bata, wata kuma kudade. bukin dai ya zama jari. Toh ku taya ni murna da addu’a, nawa na gaske ne, ni ma ranar haihuwata ta zagayo. Mu hadu mako mai zuwa!
ILLOLIN BANGAR SIYASA DA RIKICIN ZABE GA MATASA
Tabbas matasa na da muhimmancin gaske a kowacce al’umma, tasirinsu ya fi gaban a zura ido kawai ga al’amura ko yanayin yadda su ke gudanar da rayuwa. Wajibi ne da ya hau kan al’umma kan yin tattalin rayuwar matasa, samar da hanyoyin shigar da saqonnin abubuwa masu kyau don su siffantu da su, haka kuma a yi musu bayanin illolin abubuwa marasa kyau don su qaurace musu.
Duk wata qasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan ka waiwaiyi sirrin da ke tattare da samuwar wannan ci gaba, za ka ga a hannun matasansu ya ke. Saboda basu yin sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa.
Haqqi ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye da su kasance mataki na farko a inda ‘ya ‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin qasa da oda, kaucewa ayyukan barna da sauransu.
Idan iyaye su ka gaza aikata hakan ga ‘ya ‘yansu, babu tantama a dai dai lokacin da yaron ya kai shekarun girma (Matashi) ya fara mu’amala da wasu abokai a waje za su koya mishi dukkan dabi’un da su ka ga dama. A wasu lokutanma ba sai sun koya mishi ba, yanayin mu’amala a tsakaninshi da su ne zai sa ya riqa kwaikwaiyon yadda su ke tafiyar da rayuwarsu a hankali har ya gina dabi’a.
Wannan ya nuna cewa haqqin iyaye ne, kuma ikon kiyaye ‘ya ‘ya daga fadawa hadurran kwaikwayon halayen banza a waje na hannun iyayen ne. wanda idan a ka samu kaso 60% cikin 100% su na sauke wannan nauyi, za a ga chanji.
Qasashen da su ka ci gaba din nan, doka ce mai qarfi wacce ta tilasta iyaye a kan tarbiyyar ‘ya ‘yansu. Har ma idan iyayen ba su iya yi ba, sai hukuma ta dauki wannan babban aiki, saboda fahimtar irin hadarin da ke tattare da barin matasa cikin halin rashin bambance kyakkyawa da mummuna.
A qasashen Afrika, sai ya kasance kaso mai yawa na iyaye babu ruwansu da halin da ‘ya ‘yansu za su shiga idan har basu dauki nauyin kula da tarbiyyarsu ba. Haka kuma a wannan yanki namu na Afrika, iyaye da dama (sai dai kadan) ba su wani taka rawar a zo a gani wurin hobbasa kan ‘ya ‘yansu su yi karatu.
Halayen banza da aikata duk wani aiki da zai cutar da mutum ko ya janyo asarar dukiya ya na da alaqa da jahilci. Saboda shi jahilci babu abun da ya ke umurtar qwaqwalwa ta aikata face son rai da aiki ba tare da tantancewa tsakanin mai kyau da marar kyau ba.
Wannan shi ne dalilin da ya sa baragurbin ‘yan siyasa, wadanda ba burinsu ganin ci gaban Nijeriya ba, su ke amfani da matasa wurin cimma mummunar manufarsu ta aika aika. Su ne su ke ba matasan makamai da qwayoyi.
daya daga cikin abun da ke tashe a tsakankanin matasa a Nijeriya shi ne bangar siyasa da rikici. Wannan al’amari ya na da matuqar hadarin da idan ba an magance shi ba ne, lallai ba zai taba yiwuwa a mori dimokradiyya ko wanzajjen zaman lafiya ba.
A al’ummun da su ka ci gaba ba qaramin aibu bane a kira mutum da dan bangar siyasa ballantana kuma daya daga cikin masu hura wutar rikicin siyasa, amma a Nijeriya wannan ba komi ba ne. Wannan bangar siyasa ta bambanta da asalin ‘yan sara – suka da mu ke da su, da ‘yan kalare da ‘yan daba.
Duk inda a ka kira wadancan sunaye, musamman a garuruwan Bauchi, Kano da Gombe, suna ne wanda ya shafi matasa masu ayyukan rashin mutunci, rashin da’a da keta haqqoqin al’umma.
Zaben shekarar 1999, wanda tsohon janar, Olusegun Obasanjo ya lashe. Sai dai tun a wannan lokaci ne ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan rikicin zabe da bangar siyasa a tsakankanin matasa. Wannan irin mummunan dabi’a ta ci gaba da faruwa har a zaben shekarar 2003 da a ka yi. Maimakon a samu sauqe sai dai ma a ka yi ta samun qaruwar dabi’ar bangar siyasa da rikicin zabe ga matasa.
‘Yan siyasa masu mugun nufi a lokuta da dama su na aiki da matasan ne wurin sace akwatunan zabe, kai farmaki, da qone - qonen da su ka sabawa shari’a.
Yanayin da ke fuskantarmu, bisa la’akari da gabatowar babban zaben shekarar 2015, alamu na nuna matasan da ba su da ruwa da tsaki da da kalare, daba ko sara – suka akwai yiwuwar su fada ma irin wannan mummunan aiki na bangar siyasa da rikicin zabe.
A lokacin da a ka yi zaben fid da gwani na jam’iyyu a Nijeriya, an samu rahotannin yadda wasu ‘yan siyasa a jam’iyyun su ka yi amfani da matasa wurin tayar da hankula domin kawai su yi qaurin suna.
Ya kamata ne matasanmu su hankalta, su gane cewa bangar siyasa da rikicin zabe babu wani alheri da su ke haifarwa, sai dai sharruka birjik.
Rahotanni sun adana cewa a rikicin zaben shugaban qasa da ya auku a watan Afrilun 2011 ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 800, kamar yadda hukumar kare haqqin bil’adama su ka bayyana. Wadanda su ka mutu din an kashe su ne cikin kwanaki uku a jihohin arewa 11, wanda a kasha 90 na kashe – kashen matasa ne su ka aikata, haka ma rikicin zaben matasa ne su ka tayar.
Zaben shekarar 2011 da ya gabata ya tafi ya bar baya ta qura, bilhasali ma ba a taba yin zabe wanda a ka zubar da jinni kamar shi ba. An tarwatsa mutane daga muhallinsu, wasu sun rasa iyaye da ‘yan uwa. Hukumar bayar da tallafin gaggawa ta shaida cewa sama da mutane dubu 65,000 ne su ka bar gidajensu sakamakon rikicin.
Idan matasa su ka hankalta ta hanyar qauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas baragurbin ‘yan siyasa da basu son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga cimma burinsu ban a zubar jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
A matsayinka na matashi, ya kamata ne ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina rayuwarka, a samar da ayyukan da matasa za su yi bankwana da zaman banza, a samar musu guraben karatu a makarantun da mu ke da su; wannan shi ne aikin gina rayuwar mutum ba a bashi makami da qwaya ba. Makami da qwaya sai dai rusa rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da ka ke tare da su. Mu hadu mako mai zuwa!
Duk wata qasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan ka waiwaiyi sirrin da ke tattare da samuwar wannan ci gaba, za ka ga a hannun matasansu ya ke. Saboda basu yin sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa.
Haqqi ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye da su kasance mataki na farko a inda ‘ya ‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin qasa da oda, kaucewa ayyukan barna da sauransu.
Idan iyaye su ka gaza aikata hakan ga ‘ya ‘yansu, babu tantama a dai dai lokacin da yaron ya kai shekarun girma (Matashi) ya fara mu’amala da wasu abokai a waje za su koya mishi dukkan dabi’un da su ka ga dama. A wasu lokutanma ba sai sun koya mishi ba, yanayin mu’amala a tsakaninshi da su ne zai sa ya riqa kwaikwaiyon yadda su ke tafiyar da rayuwarsu a hankali har ya gina dabi’a.
Wannan ya nuna cewa haqqin iyaye ne, kuma ikon kiyaye ‘ya ‘ya daga fadawa hadurran kwaikwayon halayen banza a waje na hannun iyayen ne. wanda idan a ka samu kaso 60% cikin 100% su na sauke wannan nauyi, za a ga chanji.
Qasashen da su ka ci gaba din nan, doka ce mai qarfi wacce ta tilasta iyaye a kan tarbiyyar ‘ya ‘yansu. Har ma idan iyayen ba su iya yi ba, sai hukuma ta dauki wannan babban aiki, saboda fahimtar irin hadarin da ke tattare da barin matasa cikin halin rashin bambance kyakkyawa da mummuna.
A qasashen Afrika, sai ya kasance kaso mai yawa na iyaye babu ruwansu da halin da ‘ya ‘yansu za su shiga idan har basu dauki nauyin kula da tarbiyyarsu ba. Haka kuma a wannan yanki namu na Afrika, iyaye da dama (sai dai kadan) ba su wani taka rawar a zo a gani wurin hobbasa kan ‘ya ‘yansu su yi karatu.
Halayen banza da aikata duk wani aiki da zai cutar da mutum ko ya janyo asarar dukiya ya na da alaqa da jahilci. Saboda shi jahilci babu abun da ya ke umurtar qwaqwalwa ta aikata face son rai da aiki ba tare da tantancewa tsakanin mai kyau da marar kyau ba.
Wannan shi ne dalilin da ya sa baragurbin ‘yan siyasa, wadanda ba burinsu ganin ci gaban Nijeriya ba, su ke amfani da matasa wurin cimma mummunar manufarsu ta aika aika. Su ne su ke ba matasan makamai da qwayoyi.
daya daga cikin abun da ke tashe a tsakankanin matasa a Nijeriya shi ne bangar siyasa da rikici. Wannan al’amari ya na da matuqar hadarin da idan ba an magance shi ba ne, lallai ba zai taba yiwuwa a mori dimokradiyya ko wanzajjen zaman lafiya ba.
A al’ummun da su ka ci gaba ba qaramin aibu bane a kira mutum da dan bangar siyasa ballantana kuma daya daga cikin masu hura wutar rikicin siyasa, amma a Nijeriya wannan ba komi ba ne. Wannan bangar siyasa ta bambanta da asalin ‘yan sara – suka da mu ke da su, da ‘yan kalare da ‘yan daba.
Duk inda a ka kira wadancan sunaye, musamman a garuruwan Bauchi, Kano da Gombe, suna ne wanda ya shafi matasa masu ayyukan rashin mutunci, rashin da’a da keta haqqoqin al’umma.
Zaben shekarar 1999, wanda tsohon janar, Olusegun Obasanjo ya lashe. Sai dai tun a wannan lokaci ne ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan rikicin zabe da bangar siyasa a tsakankanin matasa. Wannan irin mummunan dabi’a ta ci gaba da faruwa har a zaben shekarar 2003 da a ka yi. Maimakon a samu sauqe sai dai ma a ka yi ta samun qaruwar dabi’ar bangar siyasa da rikicin zabe ga matasa.
‘Yan siyasa masu mugun nufi a lokuta da dama su na aiki da matasan ne wurin sace akwatunan zabe, kai farmaki, da qone - qonen da su ka sabawa shari’a.
Yanayin da ke fuskantarmu, bisa la’akari da gabatowar babban zaben shekarar 2015, alamu na nuna matasan da ba su da ruwa da tsaki da da kalare, daba ko sara – suka akwai yiwuwar su fada ma irin wannan mummunan aiki na bangar siyasa da rikicin zabe.
A lokacin da a ka yi zaben fid da gwani na jam’iyyu a Nijeriya, an samu rahotannin yadda wasu ‘yan siyasa a jam’iyyun su ka yi amfani da matasa wurin tayar da hankula domin kawai su yi qaurin suna.
Ya kamata ne matasanmu su hankalta, su gane cewa bangar siyasa da rikicin zabe babu wani alheri da su ke haifarwa, sai dai sharruka birjik.
Rahotanni sun adana cewa a rikicin zaben shugaban qasa da ya auku a watan Afrilun 2011 ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 800, kamar yadda hukumar kare haqqin bil’adama su ka bayyana. Wadanda su ka mutu din an kashe su ne cikin kwanaki uku a jihohin arewa 11, wanda a kasha 90 na kashe – kashen matasa ne su ka aikata, haka ma rikicin zaben matasa ne su ka tayar.
Zaben shekarar 2011 da ya gabata ya tafi ya bar baya ta qura, bilhasali ma ba a taba yin zabe wanda a ka zubar da jinni kamar shi ba. An tarwatsa mutane daga muhallinsu, wasu sun rasa iyaye da ‘yan uwa. Hukumar bayar da tallafin gaggawa ta shaida cewa sama da mutane dubu 65,000 ne su ka bar gidajensu sakamakon rikicin.
Idan matasa su ka hankalta ta hanyar qauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas baragurbin ‘yan siyasa da basu son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga cimma burinsu ban a zubar jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
A matsayinka na matashi, ya kamata ne ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina rayuwarka, a samar da ayyukan da matasa za su yi bankwana da zaman banza, a samar musu guraben karatu a makarantun da mu ke da su; wannan shi ne aikin gina rayuwar mutum ba a bashi makami da qwaya ba. Makami da qwaya sai dai rusa rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da ka ke tare da su. Mu hadu mako mai zuwa!
A SIYAR DA RAI A NEMO SUNA!
Haha! Matuqar ka na raye za ka yi gane – gane a duniyan nan, musamman idan ka na mu’amala da mutane barkatai, ko kuma ka na da ikon samun labarun yanayin yadda mutane daban daban daga sassan duniya su ke gudanar da rayuwarsu. A nan ne za ka tabbatarwa da kanka qarfin halin ‘yan neman suna.
Siyar da rai kala kala ne, kuma kusan masu irin wannan dabi’a ta siyar da rai sun san duk wata hanya da za su bi su aikata hakan, a wasu lokutan ta sha rutsawa da su, a wasu lokutan kuma su tsallake rijiya da baya.
Idan a ka ce siyar da rai kawai a ka yi shiru. Sai mutum ya dauka a na nufin a wurin siyar da ran dole sai ya kasance akwai barazana ga rayuwa. Wanda kuma ba haka ba ne, siyar da rai a nemo suna, ya na iya qumsar aikin da zai zubar da mutunci, qima, dattako ko ya rage kaifin wayonka a idon jama’a. wannan shi ne ma babban siyar da rai.
Wasu misalai na siyar da rai amma a ka samo sunan da a ke nema, shi ne irin qeqyashewa da tsayin dakan da tsohon mataimakin shugaban qasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi gab da zaben shekarar 2007. Inda ya fito kaitsaye ya yi fito na fito da muradin mai gidanshi, tsohon shugaban qasa Olusegun Obasanjo.
Siyar da ran da Atiku Abubakar ya yi, a na iya cewa ya ci riba, ya kuma yi suna sosai a wancan lokaci. Musamman yadda ‘yan Nijeriya su ka fara kallonshi a matsayin wani sabon gwarzo, wanda ya rusa sabuwar aqidar ‘Third Term’.
Atiku Abubakar bai tantance fada wa kasadar siyar da rai ba, har sai da ya samu tabbatattun hujjoji a kan maigidanshi Obasanjo ba zai tallafa mishi don ya maye gurbinshi ba. Sannan ya tabbatar da cewa idan har haqar ‘Third Term’’ ta cimma ruwa, shi kam sai dai kuma tarihi. Zabi biyu a wancan lokaci Alhaji Atiku Abubakar ke da su; ko dai ya danne zuciyarshi ya hadiyi haquri da duk wani wulaqanci da zai biyo baya. Ko kuma ya qaddamar da yaqi ba qaqqautawa.
A ‘yan kwanakin baya ma, siyar da ran da Malam Ibrahim Shekarau ya yi babban misali ne, saboda shi kanshi ya san ya siyar da rai ne a matakai biyu; komawa jam’iyyar PDP wacce a baya ya la’ance ta iya la’anta da abubuwan da za su biyo baya na kallon da jama’a za su riqa yi mishi. Na biyu shi ne ya zauna a cikin jam’iyyar adawa ta APC ma siyar da rai ne. bisa dalilin ita uwar jam’iyyar ta qasa ta shardanta cewa duk jihar da gwamna ko mataimakin gwamna ya komo jam’iyyar, shi ne zai zama shugabanta na jiha.
A halin da Malam Shekarau ya tsinci kanshi, ko dai ya zauna a cikin jam’iyyar ta APC qarqashin abokin adawanshi gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso ko kuma ya kama gabanshi (matakin da ya dauka). Qarshenta dai da Malam Ibrahim Shekarau ya duba da kyau, ya natsu ya ga cikin biyun, wanne siyar da rai ne zai zamar mishi mai sauqi sauqi.
Tsoron yin kasadar siyar da rai ne ya hana mutane irinsu Gwamna Sule Lamido, da Gwamna Babangida Aliyu su biye ma takwarrorinsu su Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko, Gwamna Kwankwaso da Gwamna Amaechi. Saboda ba su shirya ba, kar wurin neman suna su kwan ciki.
Wadannan su ne kadan daga cikin misalan siyar da rai a siyasance. Haka nan a mu’amalarmu ta yau da kullum, cike ta ke da siyar da rai. Musamman wadanda babban burinsu shi ne neman suna da son a ce su ne su ka yi kaza da kaza.
Wasu mutanen dabi’arsu kenan a ce su ne su ka fara aikata wani al’amari, ko su ne su ka dai daita wani abu, alhali ba za su yi nazarin me neman sunan nan zai iya janyo musu ba. Shin idan sun siyar da rai, qima da darajar da su ke kwadayi za su samu ko a’a?
Kowanne mutum mai hankali a duniyan nan, ya na da lura da kiyaye abubuwan da kan je kan dawo. Kawai yawancin abun da ke cutar da mutane a wannan zamani shi ne rashin tunani. Kyau a ce duk abun da ka riska ka tsaya ka yi tunani, ka yi nazari na musamman dangane da abun, ka tantance ka cire abubuwan da za su iya shafar mutuncinka ko qima, ko daraja, idan har akwai wadannan barazana masu yawa, sai ka yi haquri kawai.
Saboda mutunci shi ne mutum. Duk lokacin da kaso 40 cikin 100 na jama’an da ke kallonka da mutunci su ka daina, ina mai tabbatar maka da ka rasa wani babban abu a rayuwanka wanda zai yi ta janyo maka asarori na daukaka da amintan jama’a, har zuwa lokacin da za a sake sakankancewa da kai da al’amuranka.
Sau da yawa, ya fi kyautuwa ka yi shiru a abun da bai shafe ka ba. Wasu kan yi alqawuran siyar da rai, don kawai su farantawa mutum rai, alhali idan alqawarin bai cika ba, maimakon su nemo suna, sai dai su zubar da suna.
Daga qarshe ina kira ga masu dabi’ar siyar da rai don neman suna, su taimakawa kansu su rage, saboda ba kowanne siyar da ran ba ne ke tattare da suna. Wani maimakon nemo suna, sai dai ya janyo kuka da raunin da tabonshi ba zai taba gushewa ba. Mu hadu mako mai zuwa!
Siyar da rai kala kala ne, kuma kusan masu irin wannan dabi’a ta siyar da rai sun san duk wata hanya da za su bi su aikata hakan, a wasu lokutan ta sha rutsawa da su, a wasu lokutan kuma su tsallake rijiya da baya.
Idan a ka ce siyar da rai kawai a ka yi shiru. Sai mutum ya dauka a na nufin a wurin siyar da ran dole sai ya kasance akwai barazana ga rayuwa. Wanda kuma ba haka ba ne, siyar da rai a nemo suna, ya na iya qumsar aikin da zai zubar da mutunci, qima, dattako ko ya rage kaifin wayonka a idon jama’a. wannan shi ne ma babban siyar da rai.
Wasu misalai na siyar da rai amma a ka samo sunan da a ke nema, shi ne irin qeqyashewa da tsayin dakan da tsohon mataimakin shugaban qasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi gab da zaben shekarar 2007. Inda ya fito kaitsaye ya yi fito na fito da muradin mai gidanshi, tsohon shugaban qasa Olusegun Obasanjo.
Siyar da ran da Atiku Abubakar ya yi, a na iya cewa ya ci riba, ya kuma yi suna sosai a wancan lokaci. Musamman yadda ‘yan Nijeriya su ka fara kallonshi a matsayin wani sabon gwarzo, wanda ya rusa sabuwar aqidar ‘Third Term’.
Atiku Abubakar bai tantance fada wa kasadar siyar da rai ba, har sai da ya samu tabbatattun hujjoji a kan maigidanshi Obasanjo ba zai tallafa mishi don ya maye gurbinshi ba. Sannan ya tabbatar da cewa idan har haqar ‘Third Term’’ ta cimma ruwa, shi kam sai dai kuma tarihi. Zabi biyu a wancan lokaci Alhaji Atiku Abubakar ke da su; ko dai ya danne zuciyarshi ya hadiyi haquri da duk wani wulaqanci da zai biyo baya. Ko kuma ya qaddamar da yaqi ba qaqqautawa.
A ‘yan kwanakin baya ma, siyar da ran da Malam Ibrahim Shekarau ya yi babban misali ne, saboda shi kanshi ya san ya siyar da rai ne a matakai biyu; komawa jam’iyyar PDP wacce a baya ya la’ance ta iya la’anta da abubuwan da za su biyo baya na kallon da jama’a za su riqa yi mishi. Na biyu shi ne ya zauna a cikin jam’iyyar adawa ta APC ma siyar da rai ne. bisa dalilin ita uwar jam’iyyar ta qasa ta shardanta cewa duk jihar da gwamna ko mataimakin gwamna ya komo jam’iyyar, shi ne zai zama shugabanta na jiha.
A halin da Malam Shekarau ya tsinci kanshi, ko dai ya zauna a cikin jam’iyyar ta APC qarqashin abokin adawanshi gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso ko kuma ya kama gabanshi (matakin da ya dauka). Qarshenta dai da Malam Ibrahim Shekarau ya duba da kyau, ya natsu ya ga cikin biyun, wanne siyar da rai ne zai zamar mishi mai sauqi sauqi.
Tsoron yin kasadar siyar da rai ne ya hana mutane irinsu Gwamna Sule Lamido, da Gwamna Babangida Aliyu su biye ma takwarrorinsu su Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko, Gwamna Kwankwaso da Gwamna Amaechi. Saboda ba su shirya ba, kar wurin neman suna su kwan ciki.
Wadannan su ne kadan daga cikin misalan siyar da rai a siyasance. Haka nan a mu’amalarmu ta yau da kullum, cike ta ke da siyar da rai. Musamman wadanda babban burinsu shi ne neman suna da son a ce su ne su ka yi kaza da kaza.
Wasu mutanen dabi’arsu kenan a ce su ne su ka fara aikata wani al’amari, ko su ne su ka dai daita wani abu, alhali ba za su yi nazarin me neman sunan nan zai iya janyo musu ba. Shin idan sun siyar da rai, qima da darajar da su ke kwadayi za su samu ko a’a?
Kowanne mutum mai hankali a duniyan nan, ya na da lura da kiyaye abubuwan da kan je kan dawo. Kawai yawancin abun da ke cutar da mutane a wannan zamani shi ne rashin tunani. Kyau a ce duk abun da ka riska ka tsaya ka yi tunani, ka yi nazari na musamman dangane da abun, ka tantance ka cire abubuwan da za su iya shafar mutuncinka ko qima, ko daraja, idan har akwai wadannan barazana masu yawa, sai ka yi haquri kawai.
Saboda mutunci shi ne mutum. Duk lokacin da kaso 40 cikin 100 na jama’an da ke kallonka da mutunci su ka daina, ina mai tabbatar maka da ka rasa wani babban abu a rayuwanka wanda zai yi ta janyo maka asarori na daukaka da amintan jama’a, har zuwa lokacin da za a sake sakankancewa da kai da al’amuranka.
Sau da yawa, ya fi kyautuwa ka yi shiru a abun da bai shafe ka ba. Wasu kan yi alqawuran siyar da rai, don kawai su farantawa mutum rai, alhali idan alqawarin bai cika ba, maimakon su nemo suna, sai dai su zubar da suna.
Daga qarshe ina kira ga masu dabi’ar siyar da rai don neman suna, su taimakawa kansu su rage, saboda ba kowanne siyar da ran ba ne ke tattare da suna. Wani maimakon nemo suna, sai dai ya janyo kuka da raunin da tabonshi ba zai taba gushewa ba. Mu hadu mako mai zuwa!
MENENE TSORO?
Akwai wani lokaci da na je qauye a Arewacin Nijeriya, sai na yi niyyan siyan Kankana. Yayin da mai kankana ya zabo wata ‘yar babba, ya na so ya yanka, sai na lura wuqar ta yi datti sosai, na buqaci ya wanke ta tukunna. Ba tare da qyashi ba, ya tsuguna ya sa hannu a wani magudanan ruwa ya fara wanke wuqan, daga can nesa na hango yara da masu wucewa na tsayawa su tsula fitsari abunsu a magudanan ruwan.
Nan da nan na yi gaggawa na ce mishi, Malam ban ma so a yanka, kawai bani Kankanan a haka, ba tare da an yanka ba. Ina ganin wannan, wani zance na masana halayyar Jama’a ne ya fado min, inda su ke cewa, ‘Yayin da mutane su ke kallon abu a matsayin shi ne haqiqa, toh shi ne haqiqan a dukkan mu’amalolinsu.’
A dan wannan misali, mu na iya ganin yadda shi a wurin mai siyar da Kankana na qauye, bai yarda a haqiqa cewa akwai wasu qwayoyin cututtuka ba. Ni kuma da na zo daga birni na yi imanin cewa a haqiqanin gaskiya akwai qwayoyin cuta. Kuma kowanne dayya a cikinmu (tsakanina da mai kankana) mun yi aiki ne da yadda mu ka fahimci haqiqa.
Ba kawai wai ni ina da wayo ba ne ya sa na gaskata samuwar qwayoyin cututtuka, a’a, wannan ya na da alaqa da al’umman da na taso a cikinsu ne.
Wani qarin misali dangane da yadda mu ke kallon haqiqanin abu, shi ne misalin wasu tagawaye, masu suna Jack da Oscar, wadanda a ka yi rainonsu har zuwa girma a wurare daban daban. Jack an yi rainonshi a Trinidad shi kuma Oscar an raine shi a qasar Jamus.
Jack sai ya girma da qiyayyar Hitler a zuciyarshi, saboda a Trinidad ya taso. Yayin da dan uwanshi Oscar kuma ya girma da qaunar Hitler cike da zuciyanshi.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba wai abun da Hitler ya aikata ba ne asalin haqiqa. Haqiqa shi ne yadda mu ke kallon abun da shi Hitler din ya aikata.
Lokacin da a ka sace ‘yan matan makarantar Sakandare sama da 200 a garin Chibok. Yanayin yadda gwamnatin shugaban qasa Goodluck Jonathan ta riqi al’amarin ya na da fassarorida yadda kowanne mutum ko bangare na mutane za su kalle shi.
A garin Chibok da wasu yankunan Arewa, za a kalli wannan a matsayin sakaci daga shugaban qasa, saboda shi ke da ikon kiyaye duk wani dan qasa. Amma idan ka samu wani dan Neja Delta, zai iya ce ma ka babu laifi a banzantar da zancen da Shugaban Goodluck ya yi har na tsawon awanni 48, saboda bai yi imanin an sace su da gaske ba.
Masana halayyar Jama’a da zamantakewa (Sociologist) su na kiran irin wannan da yadda a ke kallo ko fassara haqiqanin al’amari. Al’umman da mu ka taso a cikinta ne ko dasa mana abubuwa da daman gaske, ciki har da yanayin yadda mu ke fahimtar haqiqanin abu. Ko mun sani ko ba mu sani ba, tasirin inda mu ka taso ne ke koyar da mu qin wani al’amari ko mutum, tare da son wani al’amari.
Wannan ba qaramin maudu’i ba ne, duk da wani na iya kallonshi a matsayin Kalmar ‘TSORO’ zalla, alhali al’amarin wuce nan.
Idan ka na so ka san menene haqinanin ma’anar tsoro, sai ka kalli Kalmar ta siffofi daban daban; idan kuwa har ka kalleta ta siffofi, za ka gamsu cewa babu wani ma’ana guda daya da ke daukan gundarin fassaran Kalmar ‘Tsoro’.
Misali, idan a ka ce abinci, ka ga ko ma dai menene, abun da ke fara zuwa a zuciyar duk wanda ya ji Kalmar shi ne, wani abu wanda zai iya yiwuwa ya shiga cikin mutum ya zauna, ko kuma ya shiga cikin a amayo shi.
Amma kawai idan a ka ce ma ka ‘Tsoro’, za ka buqaci a ba ka dama ka yi bayani, saboda shi ba yanayinsu daya da Kalmar ‘abinci’ ba. Sai a tambaye ka a ce ka fassara menene tsoro?. Ina mai tabbatar da cewa idan a ka yiwa mutum biyar wannan taambaya, amsoshinsu za su zama daban daban, amma idan ka tambaye su menene abinci, dole a amsarsu sai sun yi kamanni da juna.
Wani zai ce, tsoro shi ne firgita. Yayin da amsar wani za ta kasance, tsoro shi ne kidimewa. Wani amsan kuma na iya cewa tsoro shi ne fita daga hayyacin dai dai zuwa wani hayyaci na ba dai dai ba.
Toh idan haka ne, irin wadannan kalmomi, ta ya za mu iya fassara su ko kuma mu fahimce su yadda ya dace? Wannan ba wani abu ba ne mai wahala, ya na da sauqin gaske.
A wurin qananan Yara ‘yan qasa da shekaru 10, tsoro shi ne duk wani abu mai muni. Don haka ne ma za ka ga a lokuta da dama, irin Yaran nan masu qiriniya, sai ka ga iyayensu na ce musu ga ‘DODO’ nan. Ba wai Dodon ba ne da gaske, sannan ba wai kawai fadin Kalmar Dodon ba ne a baki, idan iyayen su k ace ga Dodo nan, sai su yi wani irin yamutse fuska ko su ma su yi wani irin firgigi yayin da su ke cewa dodon na zuwa.
Wannan yanayi da iyayen ke yi, shi ne yin tasiri a zukatan Yara, sai su gina tsoron dodo a zukatansu. Ka na iya gane tsoro a yanayin Yaro, yayin da yana yin wani abu, sai mahaifiyarshi ko mahaifinshi ya ce, ‘Ku kawo min Bulala’, a nan ba wai Kalmar bulalar b ace ke da tasiri, ta na iya yiwuwa an taba tsula ma yaron bulala, don haka qwaqwalwarshi ta kiyaye tsoron bulala.
Kaman ka kalli mutum geme – geme ne k ace mishi ga Dodo, kai ma ka san ka na batawa kanka lokaci ne. ko kuma ka kalli matashi wanda yah aura shekaru 20 zuwa sama (yana ganiyar balaga) don ya yi laifi ka ce a kawo bulala.
Tsoro a wurin matasa, shi ne kakkausan kalamai daga bakin iyayensu ko wasu wadanda su ke qimantawa. Za ka ga a lokuta da yawan gaske, idan wani abun firgici ya faru, za ka ji matashi na cewa, ‘Ni wallahi ban tsorata ba’, saboda shi a wurinshi, dar din da ya ji a cikin zuciyarshi ba sunanshi tsoro ba. Amma idan a ka kori matashi daga makarantar sakandare ko Jami’a, za ka ji ya na cewa, “Tsorona shi ne idan mahaifi ko mahaifiyata su ka sani”.
A qarshe ina so mu gane cewa, tsoro shi ne tsoro. Yadda ka fahimce shi a na ka tunanin, ya bambanta da yadda baturen Ingila ya fahimci shi. Mu hadu mako mai zuwa
Nan da nan na yi gaggawa na ce mishi, Malam ban ma so a yanka, kawai bani Kankanan a haka, ba tare da an yanka ba. Ina ganin wannan, wani zance na masana halayyar Jama’a ne ya fado min, inda su ke cewa, ‘Yayin da mutane su ke kallon abu a matsayin shi ne haqiqa, toh shi ne haqiqan a dukkan mu’amalolinsu.’
A dan wannan misali, mu na iya ganin yadda shi a wurin mai siyar da Kankana na qauye, bai yarda a haqiqa cewa akwai wasu qwayoyin cututtuka ba. Ni kuma da na zo daga birni na yi imanin cewa a haqiqanin gaskiya akwai qwayoyin cuta. Kuma kowanne dayya a cikinmu (tsakanina da mai kankana) mun yi aiki ne da yadda mu ka fahimci haqiqa.
Ba kawai wai ni ina da wayo ba ne ya sa na gaskata samuwar qwayoyin cututtuka, a’a, wannan ya na da alaqa da al’umman da na taso a cikinsu ne.
Wani qarin misali dangane da yadda mu ke kallon haqiqanin abu, shi ne misalin wasu tagawaye, masu suna Jack da Oscar, wadanda a ka yi rainonsu har zuwa girma a wurare daban daban. Jack an yi rainonshi a Trinidad shi kuma Oscar an raine shi a qasar Jamus.
Jack sai ya girma da qiyayyar Hitler a zuciyarshi, saboda a Trinidad ya taso. Yayin da dan uwanshi Oscar kuma ya girma da qaunar Hitler cike da zuciyanshi.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba wai abun da Hitler ya aikata ba ne asalin haqiqa. Haqiqa shi ne yadda mu ke kallon abun da shi Hitler din ya aikata.
Lokacin da a ka sace ‘yan matan makarantar Sakandare sama da 200 a garin Chibok. Yanayin yadda gwamnatin shugaban qasa Goodluck Jonathan ta riqi al’amarin ya na da fassarorida yadda kowanne mutum ko bangare na mutane za su kalle shi.
A garin Chibok da wasu yankunan Arewa, za a kalli wannan a matsayin sakaci daga shugaban qasa, saboda shi ke da ikon kiyaye duk wani dan qasa. Amma idan ka samu wani dan Neja Delta, zai iya ce ma ka babu laifi a banzantar da zancen da Shugaban Goodluck ya yi har na tsawon awanni 48, saboda bai yi imanin an sace su da gaske ba.
Masana halayyar Jama’a da zamantakewa (Sociologist) su na kiran irin wannan da yadda a ke kallo ko fassara haqiqanin al’amari. Al’umman da mu ka taso a cikinta ne ko dasa mana abubuwa da daman gaske, ciki har da yanayin yadda mu ke fahimtar haqiqanin abu. Ko mun sani ko ba mu sani ba, tasirin inda mu ka taso ne ke koyar da mu qin wani al’amari ko mutum, tare da son wani al’amari.
Wannan ba qaramin maudu’i ba ne, duk da wani na iya kallonshi a matsayin Kalmar ‘TSORO’ zalla, alhali al’amarin wuce nan.
Idan ka na so ka san menene haqinanin ma’anar tsoro, sai ka kalli Kalmar ta siffofi daban daban; idan kuwa har ka kalleta ta siffofi, za ka gamsu cewa babu wani ma’ana guda daya da ke daukan gundarin fassaran Kalmar ‘Tsoro’.
Misali, idan a ka ce abinci, ka ga ko ma dai menene, abun da ke fara zuwa a zuciyar duk wanda ya ji Kalmar shi ne, wani abu wanda zai iya yiwuwa ya shiga cikin mutum ya zauna, ko kuma ya shiga cikin a amayo shi.
Amma kawai idan a ka ce ma ka ‘Tsoro’, za ka buqaci a ba ka dama ka yi bayani, saboda shi ba yanayinsu daya da Kalmar ‘abinci’ ba. Sai a tambaye ka a ce ka fassara menene tsoro?. Ina mai tabbatar da cewa idan a ka yiwa mutum biyar wannan taambaya, amsoshinsu za su zama daban daban, amma idan ka tambaye su menene abinci, dole a amsarsu sai sun yi kamanni da juna.
Wani zai ce, tsoro shi ne firgita. Yayin da amsar wani za ta kasance, tsoro shi ne kidimewa. Wani amsan kuma na iya cewa tsoro shi ne fita daga hayyacin dai dai zuwa wani hayyaci na ba dai dai ba.
Toh idan haka ne, irin wadannan kalmomi, ta ya za mu iya fassara su ko kuma mu fahimce su yadda ya dace? Wannan ba wani abu ba ne mai wahala, ya na da sauqin gaske.
A wurin qananan Yara ‘yan qasa da shekaru 10, tsoro shi ne duk wani abu mai muni. Don haka ne ma za ka ga a lokuta da dama, irin Yaran nan masu qiriniya, sai ka ga iyayensu na ce musu ga ‘DODO’ nan. Ba wai Dodon ba ne da gaske, sannan ba wai kawai fadin Kalmar Dodon ba ne a baki, idan iyayen su k ace ga Dodo nan, sai su yi wani irin yamutse fuska ko su ma su yi wani irin firgigi yayin da su ke cewa dodon na zuwa.
Wannan yanayi da iyayen ke yi, shi ne yin tasiri a zukatan Yara, sai su gina tsoron dodo a zukatansu. Ka na iya gane tsoro a yanayin Yaro, yayin da yana yin wani abu, sai mahaifiyarshi ko mahaifinshi ya ce, ‘Ku kawo min Bulala’, a nan ba wai Kalmar bulalar b ace ke da tasiri, ta na iya yiwuwa an taba tsula ma yaron bulala, don haka qwaqwalwarshi ta kiyaye tsoron bulala.
Kaman ka kalli mutum geme – geme ne k ace mishi ga Dodo, kai ma ka san ka na batawa kanka lokaci ne. ko kuma ka kalli matashi wanda yah aura shekaru 20 zuwa sama (yana ganiyar balaga) don ya yi laifi ka ce a kawo bulala.
Tsoro a wurin matasa, shi ne kakkausan kalamai daga bakin iyayensu ko wasu wadanda su ke qimantawa. Za ka ga a lokuta da yawan gaske, idan wani abun firgici ya faru, za ka ji matashi na cewa, ‘Ni wallahi ban tsorata ba’, saboda shi a wurinshi, dar din da ya ji a cikin zuciyarshi ba sunanshi tsoro ba. Amma idan a ka kori matashi daga makarantar sakandare ko Jami’a, za ka ji ya na cewa, “Tsorona shi ne idan mahaifi ko mahaifiyata su ka sani”.
A qarshe ina so mu gane cewa, tsoro shi ne tsoro. Yadda ka fahimce shi a na ka tunanin, ya bambanta da yadda baturen Ingila ya fahimci shi. Mu hadu mako mai zuwa
DAN SANDA ABUN TSORO NE?
Mai karatu a wannan makon zan so in wayar da kawunanmu ne dangane da 'yan sanda da ayyukan su, za mu ta~o inda ke yiwa duk wani dan qasa na gari qaiqaiyi dangane da aikin dan sanda. Su ma na gari cikin ‘yan sandan za su qaru da fashin baqin.
Kalmar POLICE an samo ta ne daga kalmar POLITIA daga harshen Latin, su ma Latin sun samo POLITIA ne daga harshen GIRKA, domin a asali Girka sun kira Kalmar ne da POLIS.
Kafin a samar da tsarin aikin dan sanda a hukumance a wannan qasar ta mu, da ma can mu na da hanyoyin da kakanninmu su ke bi wurin samar da tsaro, kare rayuka, dukiyoyi da sauransu. Kamar misali a qasar hausa akwai DOGARAI, wadanda su ke aikin masu bayar da kariya ga Sarakuna, kuma su ke gudanar da aikin sintiri a cikin gari. A wancan lokacin SARKIN DOGARAI shi ne ke a matsayin shugaban jami'an tsaro. Cikin ayyukansu sun hada da amsar haraji, lalubowa da kuma horas da mai laifi, hana aukuwar barna da sauransu.
Haka nan kuma mutanen Masarautar SAYFAWA da su ka rayu KANEM BORNO su ma sun jima da tsarin aikin 'yan sanda a al'adance. TALBA shi ne sunan shugaban 'yan sintiri kuma alqalin alqalai a kotun MAI (sarki).
A yankin Yarabawa kuwa, yammacin Nijeriya, sunan jami'an tsaro kafin zuwan turawan mulkin mallaka sun hada da ILARI, EMESE, ko AGUNbEN su ne ke gudanar da duk wasu ayyukan 'yan sanda, ayyukansu sun yi kamanni da na DOGARAI a arewacin Nijeriya.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba bature mai jan kunne ba ne ya zo ma mutanenmu da aikin dan sanda, ba bature ba ne ya koyar da mu harkar tsaro, da tsaronmu ya zo ya same mu, sai dai ma muguntar gur~ata mana harkar tsaron da ya yi.
Zan dan ta~o yadda turawan mulkin mallaka su ka qirqiri 'yan sandan zamani, manufofin qirqirarsu da kuma sakamakon da mu ke gani har yau.
Ya na da kyau kowannenmu ya san da cewa jami'an 'yan sanda da mu ke da su a hukumance a Nijeriya, turawan mulkin mallaka ne su ka samar da su. Turawan sun fara ne da gina hukumar mutum 30 a shekarar 1861 a wurin da su ka kira 'LAGOS COLONY' wanda daga bisani wannan tsarin ya kutso yankin hausawa a shekarar 1879. A shekarar 1896 ne a ka qaddamar da jami'an 'yan sandan Legas.
A shekarar 1930 ne a ka samu hadewar jami'an 'yan sanda Arewa da na Kudu a ka samar da hukumar 'yan sanda ta qasa, kuma a ka yi mata hedikwata a Legas. A shekarar 1943 ne kuma turawan mulkin mallaka na birtaniya su ka rubutawa hukumar kundin tsari.
Na kawo wannan dan taqaitaccen tarihi ne don in yi sharar fagen yadda mai karatu zai fahimci rawar da Turawa su ka taka na samar da 'yan sanda a hukumance, kuma sun yi hakan ne ba wai don kakanninmu su ci moriyar harkar tsaro ba, ba sun yi ba ne don a kare rayuka da dukiyoyin iyayenmu.
Turawan sun kafa hukumar 'yan sanda ne saboda su samarwa kawunansu da tsaro da kariya, haka nan kuma sun kafa su ne don su riqa amfani da qarfinsu wurin danne mutane, ladabtar da wadanda ke yiwa dokokin bature kunnen qashi.
Wannan ya bamu ilmin gano dalilin da ya sa baturen mulkin mallaka ya kafa hukumar 'yan sanda, an kafa su ne su don su kare son rai da muradun mai mulki ko mai iko.
Ko da baturen mulkin mallaka ya ba Nijeriya wani abu wai shi 'yancin kai, sai ya bar wa hukumar da su ka gaje shi gadon hukumar 'yan sanda.
Shi ya sa masana da dama su na ganin cewa matuqar ana son a ga abun arziki a hukumar 'yan sandan Nijeriya, to a rushe tsarin da Bature ya assasa.
dan sanda ya kamata ne ya zama abokin kowa, ya zama mai hankali da natsuwa, ya zama mai sanin ya kamata. A halin yanzu dai akasin haka a ke gani a Nijeriya, a wasu lokutan ma sai ka ji ina ma za a riqa gwajin tabin hankali kafin a dauki mutum aikin tsaro? Saboda yadda ‘yan sanda a Nijeriya su ka dauki sakar wuta kamar kwankwadan kofin ruwa.
Bai kamata dan sanda ya zama mai girman kai, mugunta, da zafi ga jama'a ba, saboda da kudin al'umma a ke tufatar da su, a ke biyansu albashi, don su zama masu bayar da kariya ta kowacce siffa ga ‘yan qasa, ka ga kenan su hadimai ne ba su zama dodanni ba.
Idan a na son haifar da da mai ido a qoqarin samar da fahimtar juna tsakanin yan sanda da mutanen gari, dole ne a shigo da harkar 'POLICE COMMUNITY RELATIONS', ma'ana gina kyakkyawar alaqa a tsakani. Mu hadu mako mai zuwa
Kalmar POLICE an samo ta ne daga kalmar POLITIA daga harshen Latin, su ma Latin sun samo POLITIA ne daga harshen GIRKA, domin a asali Girka sun kira Kalmar ne da POLIS.
Kafin a samar da tsarin aikin dan sanda a hukumance a wannan qasar ta mu, da ma can mu na da hanyoyin da kakanninmu su ke bi wurin samar da tsaro, kare rayuka, dukiyoyi da sauransu. Kamar misali a qasar hausa akwai DOGARAI, wadanda su ke aikin masu bayar da kariya ga Sarakuna, kuma su ke gudanar da aikin sintiri a cikin gari. A wancan lokacin SARKIN DOGARAI shi ne ke a matsayin shugaban jami'an tsaro. Cikin ayyukansu sun hada da amsar haraji, lalubowa da kuma horas da mai laifi, hana aukuwar barna da sauransu.
Haka nan kuma mutanen Masarautar SAYFAWA da su ka rayu KANEM BORNO su ma sun jima da tsarin aikin 'yan sanda a al'adance. TALBA shi ne sunan shugaban 'yan sintiri kuma alqalin alqalai a kotun MAI (sarki).
A yankin Yarabawa kuwa, yammacin Nijeriya, sunan jami'an tsaro kafin zuwan turawan mulkin mallaka sun hada da ILARI, EMESE, ko AGUNbEN su ne ke gudanar da duk wasu ayyukan 'yan sanda, ayyukansu sun yi kamanni da na DOGARAI a arewacin Nijeriya.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba bature mai jan kunne ba ne ya zo ma mutanenmu da aikin dan sanda, ba bature ba ne ya koyar da mu harkar tsaro, da tsaronmu ya zo ya same mu, sai dai ma muguntar gur~ata mana harkar tsaron da ya yi.
Zan dan ta~o yadda turawan mulkin mallaka su ka qirqiri 'yan sandan zamani, manufofin qirqirarsu da kuma sakamakon da mu ke gani har yau.
Ya na da kyau kowannenmu ya san da cewa jami'an 'yan sanda da mu ke da su a hukumance a Nijeriya, turawan mulkin mallaka ne su ka samar da su. Turawan sun fara ne da gina hukumar mutum 30 a shekarar 1861 a wurin da su ka kira 'LAGOS COLONY' wanda daga bisani wannan tsarin ya kutso yankin hausawa a shekarar 1879. A shekarar 1896 ne a ka qaddamar da jami'an 'yan sandan Legas.
A shekarar 1930 ne a ka samu hadewar jami'an 'yan sanda Arewa da na Kudu a ka samar da hukumar 'yan sanda ta qasa, kuma a ka yi mata hedikwata a Legas. A shekarar 1943 ne kuma turawan mulkin mallaka na birtaniya su ka rubutawa hukumar kundin tsari.
Na kawo wannan dan taqaitaccen tarihi ne don in yi sharar fagen yadda mai karatu zai fahimci rawar da Turawa su ka taka na samar da 'yan sanda a hukumance, kuma sun yi hakan ne ba wai don kakanninmu su ci moriyar harkar tsaro ba, ba sun yi ba ne don a kare rayuka da dukiyoyin iyayenmu.
Turawan sun kafa hukumar 'yan sanda ne saboda su samarwa kawunansu da tsaro da kariya, haka nan kuma sun kafa su ne don su riqa amfani da qarfinsu wurin danne mutane, ladabtar da wadanda ke yiwa dokokin bature kunnen qashi.
Wannan ya bamu ilmin gano dalilin da ya sa baturen mulkin mallaka ya kafa hukumar 'yan sanda, an kafa su ne su don su kare son rai da muradun mai mulki ko mai iko.
Ko da baturen mulkin mallaka ya ba Nijeriya wani abu wai shi 'yancin kai, sai ya bar wa hukumar da su ka gaje shi gadon hukumar 'yan sanda.
Shi ya sa masana da dama su na ganin cewa matuqar ana son a ga abun arziki a hukumar 'yan sandan Nijeriya, to a rushe tsarin da Bature ya assasa.
dan sanda ya kamata ne ya zama abokin kowa, ya zama mai hankali da natsuwa, ya zama mai sanin ya kamata. A halin yanzu dai akasin haka a ke gani a Nijeriya, a wasu lokutan ma sai ka ji ina ma za a riqa gwajin tabin hankali kafin a dauki mutum aikin tsaro? Saboda yadda ‘yan sanda a Nijeriya su ka dauki sakar wuta kamar kwankwadan kofin ruwa.
Bai kamata dan sanda ya zama mai girman kai, mugunta, da zafi ga jama'a ba, saboda da kudin al'umma a ke tufatar da su, a ke biyansu albashi, don su zama masu bayar da kariya ta kowacce siffa ga ‘yan qasa, ka ga kenan su hadimai ne ba su zama dodanni ba.
Idan a na son haifar da da mai ido a qoqarin samar da fahimtar juna tsakanin yan sanda da mutanen gari, dole ne a shigo da harkar 'POLICE COMMUNITY RELATIONS', ma'ana gina kyakkyawar alaqa a tsakani. Mu hadu mako mai zuwa
MUTUM MUGU NE!
Mai karatu wannan makon guzuri na ke dauke da shi gare ka, wanda In Allah ya yarda ka ankare za ka ci ribar zama da duk wani mugu.
Domin shi mugu a kullum zuciyarshi ba ta san komi ba face kanshi, babu ruwanshi da wadanda ke qarqashinsa, bilhasali ma ba ya qaunar ci gabansu don a tsammanin busasshiyar zuciyarsa za su iya yin kafada da kadada da shi, kun ji bahaguwar fikira.
Mutum ne zai ingiza ka wurin aikata wani aiki, wanda har cikin zuciyarshi, tsakaninshi da Allah ya san wannan aikin ba alheri ba ne amma saboda ka cutu zai rintse ido a kan yi maka ingiza mai kantu wuta. Musamman a al’amuran da su ka shafi kasuwanci, cinikayya, miqa amana, qulla aure da sauransu.
Faram-faram cikin fara’a za ka ga mutum ya na tarairayarka, mutumin kirki a fuska amma kuma mamugunci a zuci. A yi ta nan da nan da kai, alhali kuma ba a son duk wani abu da zai alamta nasara ko daukakarka.
Me a ke nufi da mugunta?, za a iya samun fassarori mabambanta dangane da kalmar ‘Mugunta’, amma abin la’akari shi ne ko ta wacce siga ka fassara Kalmar zai kasance ta na alamta wani abu ne mara kyau.
Masana halayyar jama’a su na fassara Kalmar ‘Mugunta’ a matsayin dabi’a wacce ke tattare da rayuwar mutane, dabi’a ce wacce kowanne mutum ya na da ita, sai dai mutum ya na iya magance dabi’ar da wasu dabi’un. Akwai muhawara sosai akan wannan fassarar.
Mugunta ta na farawa ne a hankali sakamakon ‘Son rai’, shi kuwa son rai ya samo asali ne daga fargabar kubucewar iko daga hannu, sannan gazawa ne ga wanda ke aikatawa.
Babban alamin mai son rai shi ne wanda ya ke gabato da buqatunshi gaba-gaba, ko da kuwa akwai wadanda su ka fi shi matsuwa da damuwa.
Sai dai kuma a na iya cewa dabi’ar mugunta na iya samo asali daga yarintar da mutum ya yi. idan a lokacin yarinta, mutum bai samu tarbiyyar da ta dace ba a wurin iyayenshi, lallai dabi’ar mugunta na iya yin tasiri akanshi. Saboda mu’amalolin da zai yi da wasu yaran a waje, za su iya kasancewa masu mugayen dabi’u.
Dadin dadawa kuma, mugunta na iya samo asali daga gidan da a ka samu sabani tsakanin iyaye ‘Broken home’ har ta kai ga aure ya rabu. A irin wannan halin mutum ba zai samu tagomashin tasowa tare da cikakkun Iyaye ba. Idan ya tsammaci mahaifinshi ya cuci mahaifiyarshi ne, shi kenan dabi’ar mugunta ta fara samun muhalli a zuciyarshi.
Wasu mutanen kuma mugaye ne saboda su na so su janyo hankalin al’umma zuwa ga halin da su ke ciki. Irin wadanda a ka yi biris da su ba a nuna musu qauna. Kamar misalin masu shaye shayen kayan maye, idan ba a dauki matakin janyo su a jiki da kwakkwafa su ba, za su yi ta aikata dabi’o’in mugunta don su janyo hankalin al’umma.
Sannan kuma akwai kason wasu mugayen mutane guda biyu; na farko shi ne wanda ke ganin shi ya fi qarfin kowa, akwai kuma wanda ke ganin shi wulaqantacce ne.
Mafi sharrin shi ne mugun da ke ganin ya fi qarfin kowa, kuma mutane duk a qasanshi ya kamata a ce su ke, wannan ya fi zafafawa a mugunta, saboda duk wata hanya da wani zai ci gaba toshe ta ya ke yi, kuma babu abun da ya ke qauna a duniya irin a ce ya danqwafar da wasu a qarqashinsa ya na bautar da su kaman bayi.
Shi kuwa mugun da ke ganin shi wulaqantacce ne ya fi kowa wawanci, saboda shi a ganinshi a komi an barshi baya, zai kasance ya na qasqantar da kanshi kuma ya na jin nauyin yin mu’amala da mutane saboda ya na ganin bai kai ba. Don haka ne sai ya riqa yi wa mutane mugunta, don a tunaninshi sun fi shi.
Sai dai fa babu abun da ya kai maganin mugu sauqi a wannan rayuwa, kawai mutum na buqatar ya san hanyoyin da zai bi ne. Da zaran ka fahimci cewa wani mugu ne, ka yi qoqarin sauya mu’amala da shi, duk abun da za ka aikata kar ka barshi ya yi tsammanin shi ke iko da rayuwarka.
Ba wai ina nufin ka watsar da shi ba ne, a’a, kawai ka yi qoqarin yin mu’amala da shi kamar yadda ka ke yi da sauran mutane, da kanshi za ka ga ya fara canzawa, saboda ya fara fahimtar ka san ciwon kanka, ci gaba da danne ka ba zai yiwu ba.
A kowanne mataki na rayuwa sai ka hadu da mugu. [alibai sun san me na ke nufi da mugu, musamman wadanda su ke haduwa da ‘yan baqin ciki qiri - qiri, wadanda ke bata rai kawai saboda wani ya fi su sakamako mai kyau.
Haka nan ‘yan kasuwa ma sun san mugu, saboda shi ne ke surkule, tsafe tsafe da kauce hanya don kawai ya ga jarin wani ya rushe. Kusan a manyan kasuwanni, sai dai ka yi ta ganin a na ajiyewa mutane Manja da doya a qofar shago, don tsabar mugunta!
A kowacce ma’aikata akwai mugu, a wasu lokutan mugun na nan kwance cikin ma’aikatar wani lokaci kuma ya na bibiyan ayyukan ma’aikatar ne ya na kai tsegumi don a kori wani daga aikin da ya ke cin abinci.
Mugu bai so ya ga a na dariya, bai so ya ga a na walwala, bai so ya ga mutane na zumunci cikin annushuwa. Komi na jin dadin duniya ya fi so su zama na shi. Kuma mugu shi burinshi shi ne kullum mutane su riqa roqonshi da neman taimako a wurinshi. Allah dai wadaran Mugu.
Wani mahaukaci da na sani a unguwarmu, idan ya zo wucewa ka ce ‘Mutum Mugu ne’, caraf za ka ji ya amsa; ‘Ko ya mutu sai an daure shi’. Mu hadu mako mai zuwa
Domin shi mugu a kullum zuciyarshi ba ta san komi ba face kanshi, babu ruwanshi da wadanda ke qarqashinsa, bilhasali ma ba ya qaunar ci gabansu don a tsammanin busasshiyar zuciyarsa za su iya yin kafada da kadada da shi, kun ji bahaguwar fikira.
Mutum ne zai ingiza ka wurin aikata wani aiki, wanda har cikin zuciyarshi, tsakaninshi da Allah ya san wannan aikin ba alheri ba ne amma saboda ka cutu zai rintse ido a kan yi maka ingiza mai kantu wuta. Musamman a al’amuran da su ka shafi kasuwanci, cinikayya, miqa amana, qulla aure da sauransu.
Faram-faram cikin fara’a za ka ga mutum ya na tarairayarka, mutumin kirki a fuska amma kuma mamugunci a zuci. A yi ta nan da nan da kai, alhali kuma ba a son duk wani abu da zai alamta nasara ko daukakarka.
Me a ke nufi da mugunta?, za a iya samun fassarori mabambanta dangane da kalmar ‘Mugunta’, amma abin la’akari shi ne ko ta wacce siga ka fassara Kalmar zai kasance ta na alamta wani abu ne mara kyau.
Masana halayyar jama’a su na fassara Kalmar ‘Mugunta’ a matsayin dabi’a wacce ke tattare da rayuwar mutane, dabi’a ce wacce kowanne mutum ya na da ita, sai dai mutum ya na iya magance dabi’ar da wasu dabi’un. Akwai muhawara sosai akan wannan fassarar.
Mugunta ta na farawa ne a hankali sakamakon ‘Son rai’, shi kuwa son rai ya samo asali ne daga fargabar kubucewar iko daga hannu, sannan gazawa ne ga wanda ke aikatawa.
Babban alamin mai son rai shi ne wanda ya ke gabato da buqatunshi gaba-gaba, ko da kuwa akwai wadanda su ka fi shi matsuwa da damuwa.
Sai dai kuma a na iya cewa dabi’ar mugunta na iya samo asali daga yarintar da mutum ya yi. idan a lokacin yarinta, mutum bai samu tarbiyyar da ta dace ba a wurin iyayenshi, lallai dabi’ar mugunta na iya yin tasiri akanshi. Saboda mu’amalolin da zai yi da wasu yaran a waje, za su iya kasancewa masu mugayen dabi’u.
Dadin dadawa kuma, mugunta na iya samo asali daga gidan da a ka samu sabani tsakanin iyaye ‘Broken home’ har ta kai ga aure ya rabu. A irin wannan halin mutum ba zai samu tagomashin tasowa tare da cikakkun Iyaye ba. Idan ya tsammaci mahaifinshi ya cuci mahaifiyarshi ne, shi kenan dabi’ar mugunta ta fara samun muhalli a zuciyarshi.
Wasu mutanen kuma mugaye ne saboda su na so su janyo hankalin al’umma zuwa ga halin da su ke ciki. Irin wadanda a ka yi biris da su ba a nuna musu qauna. Kamar misalin masu shaye shayen kayan maye, idan ba a dauki matakin janyo su a jiki da kwakkwafa su ba, za su yi ta aikata dabi’o’in mugunta don su janyo hankalin al’umma.
Sannan kuma akwai kason wasu mugayen mutane guda biyu; na farko shi ne wanda ke ganin shi ya fi qarfin kowa, akwai kuma wanda ke ganin shi wulaqantacce ne.
Mafi sharrin shi ne mugun da ke ganin ya fi qarfin kowa, kuma mutane duk a qasanshi ya kamata a ce su ke, wannan ya fi zafafawa a mugunta, saboda duk wata hanya da wani zai ci gaba toshe ta ya ke yi, kuma babu abun da ya ke qauna a duniya irin a ce ya danqwafar da wasu a qarqashinsa ya na bautar da su kaman bayi.
Shi kuwa mugun da ke ganin shi wulaqantacce ne ya fi kowa wawanci, saboda shi a ganinshi a komi an barshi baya, zai kasance ya na qasqantar da kanshi kuma ya na jin nauyin yin mu’amala da mutane saboda ya na ganin bai kai ba. Don haka ne sai ya riqa yi wa mutane mugunta, don a tunaninshi sun fi shi.
Sai dai fa babu abun da ya kai maganin mugu sauqi a wannan rayuwa, kawai mutum na buqatar ya san hanyoyin da zai bi ne. Da zaran ka fahimci cewa wani mugu ne, ka yi qoqarin sauya mu’amala da shi, duk abun da za ka aikata kar ka barshi ya yi tsammanin shi ke iko da rayuwarka.
Ba wai ina nufin ka watsar da shi ba ne, a’a, kawai ka yi qoqarin yin mu’amala da shi kamar yadda ka ke yi da sauran mutane, da kanshi za ka ga ya fara canzawa, saboda ya fara fahimtar ka san ciwon kanka, ci gaba da danne ka ba zai yiwu ba.
A kowanne mataki na rayuwa sai ka hadu da mugu. [alibai sun san me na ke nufi da mugu, musamman wadanda su ke haduwa da ‘yan baqin ciki qiri - qiri, wadanda ke bata rai kawai saboda wani ya fi su sakamako mai kyau.
Haka nan ‘yan kasuwa ma sun san mugu, saboda shi ne ke surkule, tsafe tsafe da kauce hanya don kawai ya ga jarin wani ya rushe. Kusan a manyan kasuwanni, sai dai ka yi ta ganin a na ajiyewa mutane Manja da doya a qofar shago, don tsabar mugunta!
A kowacce ma’aikata akwai mugu, a wasu lokutan mugun na nan kwance cikin ma’aikatar wani lokaci kuma ya na bibiyan ayyukan ma’aikatar ne ya na kai tsegumi don a kori wani daga aikin da ya ke cin abinci.
Mugu bai so ya ga a na dariya, bai so ya ga a na walwala, bai so ya ga mutane na zumunci cikin annushuwa. Komi na jin dadin duniya ya fi so su zama na shi. Kuma mugu shi burinshi shi ne kullum mutane su riqa roqonshi da neman taimako a wurinshi. Allah dai wadaran Mugu.
Wani mahaukaci da na sani a unguwarmu, idan ya zo wucewa ka ce ‘Mutum Mugu ne’, caraf za ka ji ya amsa; ‘Ko ya mutu sai an daure shi’. Mu hadu mako mai zuwa
MUTUM DA QWAQWALWARSA!
A yanzu a duniya babu wani fanni da ke amsuwa fiye da fannin ilmin sanin halayyan dan Adam da qwaqwalwarsa. Wannan fanni wanda a turance a ke kiranshi da ‘Psychology’ ya na a sahun gaba cikin fannonin da su ke tashe. Haka kuma wadanda su ka karanta fannin sun fi saurin samun ayyuka; wadanda su ka hada da ayyukan wucin gadi, aikin din din din, da sauransu.
Wata qila mutum ya ce ai fannin ilmin akawu ‘Accounting’ shi ne mafi amsuwa da saurin samarwa mutum gurbin aiki. Eh, ba zan yi jayayya ba idan dan Nijeriya ya ce haka (dan Nijeriyan ma wanda bai san me ke tafiya a duniya ba), saboda a Nijeriya hukumomin da su ka gabata ba su dauki qwaqwalwar dan adam da muhimmanci ba. Babbar damuwarsu ita ce a qirga a kwashe, sai kuma a lissafa.
Amma idan mutum ya na bibiyan abubuwan da ke faruwa a qasashen da su ka ci gaba, qasashen da su ka dauki rayuwar mutanensu da muhimmanci, za ka samu cewa sun mayar da hankali sosai ga wadannan fannoni guda biyu; fannin kiwon lafiya da maganguna, da kuma fannin halayyar dan adam da qwaqwalwa.
Da yawan mutane na tsintar kawunansu a cikin matsalar qwaqwalwa wanda a qashin kansu ba za su iya yin cikakken bayanin me ke damunsu ba, haka kuma ba su san daga ina su ka yi gamo da wannan cuta ba. Da yawan ‘yan Nijeriya na fama da irin wannan. Mutum na da cuta a qwaqwalwarsa, amma bai ma san da zamanta ba.
Akwai wani masani da na ji ya na qalubalantar likitoci a kan matuqar su na buqatar aikinsu ya riqa tafiya lafiya qalau, wajibi ne su samu tarbiyya daga masana halayyan dan Adam da qwaqwalwa ko kuma ma ya kasance kowanne asibiti akwai sashen da ke wannan aiki.
Na yarda da zancen masanin, saboda a qasashen da su ka ci gaba, ba kowacce cuta ba ce a ke barin mai ita a hannun likitoci. Saboda a sau da yawa matsalar na da alaqa ne da qwaqwalwa. Aiki ne na masana wadanda su ka qware a sanin yadda matsalolin qwaqwalwar mutum da yadda ya kamata ta kasance. Masana a wannan fanni, su kan yi la’akari da damuwa, fargaba, qunci, da sauransu don bayar da shawara ga mutum.
Hadari ne sosai idan mutum ya na cikin damuwa amma kuma ya kasance ya na hadiye damuwar a cikinshi. Yawanci mutane masu irin dabi’ar nan ta shiru shiru (rashin son yin magana) sun fi fadawa wannan hadari. Saboda haka ne akwai wasu masana halayyar dan Adam da qwaqwalwa wadanda a ke kira da ‘Counseling Psychologist’, babban aikinsu shi ne su koyawa mutum yadda zai iya yin magana cikin mutane, yadda za ka iya fadin ra’ayinka, ka amayar da abin da ke cikin cikinka ba tare da wani boye boye ba.
A lokuta da daman gaske an fi samun wadanda su ka qware a fannin kwakkwafa tunanin mutum don ya iya magana a asibitocin lura da masu cutar qwaqwalwa, manyan asibitoci har ma da makarantu. A qasashen da su ka ci gaba a na samarwa da makarantun Firamare irin wadannan qwararru ne saboda su riqa lura da yanayin dalibai yara. Saboda a sau da yawa akwai yaara haziqai amma ba su iya yin magana ko su fuskanci al’umma domin bayyana hazaqarsu.
Wuce nan ma, ya na daga cikin aikin irin wadancan qwararru shiga tsakani don sansanta ma’aurata a al’amuran da ke buqatar shawarwarin hankali, tunani, qwaqwalwa da sauransu. Idan da a yankin Arewacin Nijeriya ma’aurata za su riqa neman shawarwarin irin wadannan qwararru ba tare da gaggauta yanke hukunci ba, da an samu sauqi a yawaitar mutuwar auren da mu ke fama da ita, da zawarawa sun yi qaranci.
Akwai nau’in mutanen da ke fama da gurbatar qwaqwalwa, ba dole sai al’amarin ya kai su ga bin bola ko titi ba, ba dole sai sun fara buge buge ko zare idanu ba. Wani ya na da irin wannan cutar, amma saboda rashin neman shawarar masana a hankali za ta yi ta girma daga qarama zuwa babba.
Kai da kanka idan ka aikata wani aikin, har cikin zuciyarka ka san ka na buqatar likitan qwaqwalwa. Gurbatar qwalqwalwa ne ke sa mutum ya riqa sawwala cewa abun da ba zai yiwu ba zai iya yiwuwa, kamar mutum ya fara tunanin idan ya sa tafin hannunshi zai iya hana hasken rana bayyana. Ko kuma mutum ya na da ‘ya ‘ya, sai ya riqa nuna fifiko a bayyane a tsakanin ‘ya ‘yan, kuma har ta kai ‘ya ‘yan su fahimci fifikon; wannan ma matsala ce ta qwaqwalwa wacce mutum ke buqatar masana ‘Clinical Psychologist’ su yi mishi bayanin mafita don a magance ta.
Mafi burgewa a wannan fanni shi ne fannin da qwararru ke son sanin yadda mutane ke aikata wata dabi’a, kuma don me su ke aikatawa a cikin al’umma. Wannan sashe shi ne a ke kira da ‘Social Psychology’. ta ya za ka iya tasiri a dabi’ar mutane, haka nan kuma ta wanne siffa dabi’arsu za ta iya tasiri a kanka?
A taqaice dai a nan akwai abubuwa guda biya, su ne; matuqar akwai mutane a tare da kai, tsaf za su iya yin tasiri a dabi’unka. Na biyu a dai dai lokacin da qwaqwalwarka ta iya tantance cewa akwai mutane a wurin da ka ke nan ma kasantuwarsu zai canza dabi’arka.
Kamar misali, idan ka je gidan surukanka (iyayen matarka), yanayin yadda za ka natsu ka riqa bin komi sannu a hankali zai saba da yadda za ka riqa yin abubuwa yayin da ka ke tsakiyar gidan iyayenka.
Wannan misali ya nuna kenan kasantuwar a gidan surukanka ka kawo a qwaqwalwarka cewa akwai iyayen matarka, ‘yan uwanta maza ko mata, wannan zai sa ka tilastawa dabi’arka domin yin komi yadda ya dace. Amma idan da a ce a gidan surukan na ka, sai ka samu tabbacin cewa babu kowa a gidan, duk sun yi tafiya, a irin wannan yanayi z aka saki jiki ne ka aikata duk wata dabi’ar da ita ce asalin dabi’arka. Mu hadu a mako mai zuwa!
Wata qila mutum ya ce ai fannin ilmin akawu ‘Accounting’ shi ne mafi amsuwa da saurin samarwa mutum gurbin aiki. Eh, ba zan yi jayayya ba idan dan Nijeriya ya ce haka (dan Nijeriyan ma wanda bai san me ke tafiya a duniya ba), saboda a Nijeriya hukumomin da su ka gabata ba su dauki qwaqwalwar dan adam da muhimmanci ba. Babbar damuwarsu ita ce a qirga a kwashe, sai kuma a lissafa.
Amma idan mutum ya na bibiyan abubuwan da ke faruwa a qasashen da su ka ci gaba, qasashen da su ka dauki rayuwar mutanensu da muhimmanci, za ka samu cewa sun mayar da hankali sosai ga wadannan fannoni guda biyu; fannin kiwon lafiya da maganguna, da kuma fannin halayyar dan adam da qwaqwalwa.
Da yawan mutane na tsintar kawunansu a cikin matsalar qwaqwalwa wanda a qashin kansu ba za su iya yin cikakken bayanin me ke damunsu ba, haka kuma ba su san daga ina su ka yi gamo da wannan cuta ba. Da yawan ‘yan Nijeriya na fama da irin wannan. Mutum na da cuta a qwaqwalwarsa, amma bai ma san da zamanta ba.
Akwai wani masani da na ji ya na qalubalantar likitoci a kan matuqar su na buqatar aikinsu ya riqa tafiya lafiya qalau, wajibi ne su samu tarbiyya daga masana halayyan dan Adam da qwaqwalwa ko kuma ma ya kasance kowanne asibiti akwai sashen da ke wannan aiki.
Na yarda da zancen masanin, saboda a qasashen da su ka ci gaba, ba kowacce cuta ba ce a ke barin mai ita a hannun likitoci. Saboda a sau da yawa matsalar na da alaqa ne da qwaqwalwa. Aiki ne na masana wadanda su ka qware a sanin yadda matsalolin qwaqwalwar mutum da yadda ya kamata ta kasance. Masana a wannan fanni, su kan yi la’akari da damuwa, fargaba, qunci, da sauransu don bayar da shawara ga mutum.
Hadari ne sosai idan mutum ya na cikin damuwa amma kuma ya kasance ya na hadiye damuwar a cikinshi. Yawanci mutane masu irin dabi’ar nan ta shiru shiru (rashin son yin magana) sun fi fadawa wannan hadari. Saboda haka ne akwai wasu masana halayyar dan Adam da qwaqwalwa wadanda a ke kira da ‘Counseling Psychologist’, babban aikinsu shi ne su koyawa mutum yadda zai iya yin magana cikin mutane, yadda za ka iya fadin ra’ayinka, ka amayar da abin da ke cikin cikinka ba tare da wani boye boye ba.
A lokuta da daman gaske an fi samun wadanda su ka qware a fannin kwakkwafa tunanin mutum don ya iya magana a asibitocin lura da masu cutar qwaqwalwa, manyan asibitoci har ma da makarantu. A qasashen da su ka ci gaba a na samarwa da makarantun Firamare irin wadannan qwararru ne saboda su riqa lura da yanayin dalibai yara. Saboda a sau da yawa akwai yaara haziqai amma ba su iya yin magana ko su fuskanci al’umma domin bayyana hazaqarsu.
Wuce nan ma, ya na daga cikin aikin irin wadancan qwararru shiga tsakani don sansanta ma’aurata a al’amuran da ke buqatar shawarwarin hankali, tunani, qwaqwalwa da sauransu. Idan da a yankin Arewacin Nijeriya ma’aurata za su riqa neman shawarwarin irin wadannan qwararru ba tare da gaggauta yanke hukunci ba, da an samu sauqi a yawaitar mutuwar auren da mu ke fama da ita, da zawarawa sun yi qaranci.
Akwai nau’in mutanen da ke fama da gurbatar qwaqwalwa, ba dole sai al’amarin ya kai su ga bin bola ko titi ba, ba dole sai sun fara buge buge ko zare idanu ba. Wani ya na da irin wannan cutar, amma saboda rashin neman shawarar masana a hankali za ta yi ta girma daga qarama zuwa babba.
Kai da kanka idan ka aikata wani aikin, har cikin zuciyarka ka san ka na buqatar likitan qwaqwalwa. Gurbatar qwalqwalwa ne ke sa mutum ya riqa sawwala cewa abun da ba zai yiwu ba zai iya yiwuwa, kamar mutum ya fara tunanin idan ya sa tafin hannunshi zai iya hana hasken rana bayyana. Ko kuma mutum ya na da ‘ya ‘ya, sai ya riqa nuna fifiko a bayyane a tsakanin ‘ya ‘yan, kuma har ta kai ‘ya ‘yan su fahimci fifikon; wannan ma matsala ce ta qwaqwalwa wacce mutum ke buqatar masana ‘Clinical Psychologist’ su yi mishi bayanin mafita don a magance ta.
Mafi burgewa a wannan fanni shi ne fannin da qwararru ke son sanin yadda mutane ke aikata wata dabi’a, kuma don me su ke aikatawa a cikin al’umma. Wannan sashe shi ne a ke kira da ‘Social Psychology’. ta ya za ka iya tasiri a dabi’ar mutane, haka nan kuma ta wanne siffa dabi’arsu za ta iya tasiri a kanka?
A taqaice dai a nan akwai abubuwa guda biya, su ne; matuqar akwai mutane a tare da kai, tsaf za su iya yin tasiri a dabi’unka. Na biyu a dai dai lokacin da qwaqwalwarka ta iya tantance cewa akwai mutane a wurin da ka ke nan ma kasantuwarsu zai canza dabi’arka.
Kamar misali, idan ka je gidan surukanka (iyayen matarka), yanayin yadda za ka natsu ka riqa bin komi sannu a hankali zai saba da yadda za ka riqa yin abubuwa yayin da ka ke tsakiyar gidan iyayenka.
Wannan misali ya nuna kenan kasantuwar a gidan surukanka ka kawo a qwaqwalwarka cewa akwai iyayen matarka, ‘yan uwanta maza ko mata, wannan zai sa ka tilastawa dabi’arka domin yin komi yadda ya dace. Amma idan da a ce a gidan surukan na ka, sai ka samu tabbacin cewa babu kowa a gidan, duk sun yi tafiya, a irin wannan yanayi z aka saki jiki ne ka aikata duk wata dabi’ar da ita ce asalin dabi’arka. Mu hadu a mako mai zuwa!
BABBAR MAGANA: Yadda a ke gina dabi’a
Akwai abubuwa da yawan gaske wadanda su ne ke haifar da dabi’a ko su yi tasiri a kan dabi’un jama’a. irin wadannan abubuwa su na da yawan gaske, amma wadanda na ke son na yi tsokaci a kansu, su ne mafiya tasiri kuma wadanda ke kan gaba.
Ya na da kyau mutane su san cewa babu yadda za a yi a samu wata dabi’a wacce ba za a iya bayanin musabbabinta ba, ko kuma dabi’ar da za a ce babu wasu dalilai da suka tasirantu wurin samuwarta.
A wurin masana halayyar jama’a da zamantakewa, babu wani abu da ya kai matsugunin al’umma muhimmanci da tasiri. Saboda maganar gaskiya ita ce, duk wanda ya ce shi zai qauracewa zama a cikin al’umma ko qauracewa mu’amala da su, babu makawa zai tsinci kanshi a rayuwar kadaici, wanda daga nan zai fara aikata dabi’un da su ka saba da na mutane.
Kamar yadda Masani Emile Durkheim (1858 – 1917) ya ke fadi, ‘Society is sui generis’, ma’ana matsugunin al’umma ya na da tasiri da qarfin gaske fiye da qarfin ikon dan Adam.
Wani qarin haske a nan shi ne; mutum na iya yin tasiri wurin sauya dabi’un wasu mutane, amma a bangare guda kuma wannan mutumin babu yadda za a yi ya iya yin tasiri ga al’umma. Ko da a aikata ayyukan alheri ne, duk dagewarka, sai dai ka iya sauya dabi’ar kaso mai yawa, amma ba zai yiwu ka sauya komi da kowa, tsarin gudanarwa, da kuma cibiyoyi da bangarorin al’umma ba.
A lokuta da dama mutane na boye haqiqanin dabi’arsu don dai kawai su yi tasiri a zukatan wasu. A iya fahimtar masana halayyar jama’a da zamantakewa, don kawai ka ga mutum ya na yi maka murmushi, hakan ba ya na nufin murmushin qauna ko shauqi ba ne, wannan murmushin na buqatar fassara. Babu kuma yadda za a yi ka samu fassara wannan murmushi har sai ka yi mu’amala da wanda ya ke yi maka murmushin, sannan za ka san haqiqanin dalili.
Ta na iya yiwuwa me yin murmushin ya na so ne ya assasa wani tubalin abota a tsakaninka da shi, a wata mahangar kuma ta na iya yiwuwa me murmushin ya yi ne saboda ya shaidi fuskarka a wani wuri daban.
Matakin da za ka dauka bayan baquwar fuska ta yi maka murmushi ne zai samar da mafita ga murmushin. Misali idan bayan ya yi maka murmushi, sai kai ma ka mayar da murmushi, wannan zai isarwa da baqon fuskar saqon cewa ka aminta da murmushin da ya yi maka. Idan kuma mai neman a qulla abota ne, zai samu wata damar da zai gabatar da muradinshi.
Amma a dai dai lokacin da mutum ya ganka ya yi murmushi, sai ka murtuqe fuska, ko ma da me wannan me murmushin ya zo, zai samu cikas da sacewar gwiwa a yunqurinshi.
Ya na da kyau mu fahimci cewa a lokuta da dama idan mutum ya yi maka murmushi, ba ya na nufin murmushin farin ciki ba ne, wani murmushin na tashin hankali ne, wani murmushin na masifa ne, wani murmushin na mugunta da qeta ne. don haka fahimtar wanne irin murmushi ne baquwar fuska ta yi mana, dole ne mu natsu, mu fahimci a wanne yanayi ne a ka yi murmushin, shin ya dace da yanayin da za a yi murmushi ko a’a. ya fasalin me murmushin ya ke, shin ya yi kama da masu sakakkiyar fuskar da ta saba yin murmushi?
Sai na biyu, wurin da mu ke zaune (inda mu ke rayuwa) ya na da muhimmancin gaske ga dabi’unmu. Akwai wani bincike da wani masani mai suna Anderson ya gudanar a shekarar 1997, wanda bayan ya kammala ne ya fitar da natijar cewa, ‘Yanayin zafi na iya samar da dabi’ar mugunta, fushi, da zafin rai ga mutane’.
Abin da ya ke nufi shi ne wuraren da ke fama da matsanancin zafi na yanayi, wannan zafin na iya sawa a yi ta samun mutane masu dabi’u masu tsananin gaske.
Hatta wurin da mu ke zama, muhallinmu ya na taka muhimmiyar rawa a dabi’unmu. Ka kwatanta dabi’ar mutumin da ke kwana a cikin daki, na’urar bayar da iska na sanyaya shi, sannan akwai katifa da matashin kai mai laushi; da kuma mutumin da ke kwana a bakin bola, ruwan kwacami da kwadi na shagalinsu a gefenshi. Za ka samu hatta yanayin yadda wadannan mutane biyu ke tunani ya bambanta, haka kuma za ka ga dabi’unsu sun bambanta sosai. Dole dai shi makusancin bola ya ginu da dabi’ar son doyi, dauda da duk wani nau’insu.
Na uku, al’adunmu na da muhimmancin gaske a wurin gina dabi’ar dan Adam. Al’adarka a lokuta da dama ke gina ma dabi’ar qin wasu abubuwa, al’ada ke gina ma dabi’ar sanya tufafi nau’I kaza tare da gujewa nau’I kaza. Al’adarka ke gina maka dabi’ar qin aminta da abota da wasu nau’in mutane, tare da aminta da abotar wasu nau’in.
Daga qarshe, duk da akwai wasu abubuwa da daman gaske wadanda ke gina dabi’ar dan adam, amma zan so na taqaita ga yadda yanayin qirar halitta ke tasiri ga dabi’unmu.
Allah kan halicci mutane daban daban, wasu a yi su manya da babban jiki, wasu masu fadin qirji, wasu farare, wasu baqaqe. Wasu kyawawa wasu munana. Wasu sirara wasu masu qiba.
Babban misalin yadda qirar mutum ke tasiri ga dabi’armu shi ne; yadda a wasu yankunan qasar nan a ka samu ginuwar dabi’ar qwallafa rai ga farar mace. Yanayin yadda a ke son farar macen ma har ya baci, wannan ya sanya a ka samu sauyi a dabi’un musamman MATA a yanzu, ta yadda duk baqin mace sai kawai ta gina dabi’ar yin amfani da mai me sauya launin fata.
Wannan dabi’a ta amfani da me mai sauya launin fata ya ginu ne ya kuma tasirantu a zukatan mata sakamakon mayar da hankali da su ka ga maza su ke yi ga dole sai farar mace. Wannan wauta da rashin tunanin da wasu mazan kan yi dangane da wuce gona da iri wurin son farar mace, ya janyowa al’umma asara me yawan gaske, tare da haifar da wata dabi’ar tir ta sauya launin fata. Haka kuma aure sai ya zama ba a na bin diddigin tarbiyya da asali ba ne, saboda sun ce su na son ‘Fara ko aljana ce’. mu hadu mako mai zuwa.
Ya na da kyau mutane su san cewa babu yadda za a yi a samu wata dabi’a wacce ba za a iya bayanin musabbabinta ba, ko kuma dabi’ar da za a ce babu wasu dalilai da suka tasirantu wurin samuwarta.
A wurin masana halayyar jama’a da zamantakewa, babu wani abu da ya kai matsugunin al’umma muhimmanci da tasiri. Saboda maganar gaskiya ita ce, duk wanda ya ce shi zai qauracewa zama a cikin al’umma ko qauracewa mu’amala da su, babu makawa zai tsinci kanshi a rayuwar kadaici, wanda daga nan zai fara aikata dabi’un da su ka saba da na mutane.
Kamar yadda Masani Emile Durkheim (1858 – 1917) ya ke fadi, ‘Society is sui generis’, ma’ana matsugunin al’umma ya na da tasiri da qarfin gaske fiye da qarfin ikon dan Adam.
Wani qarin haske a nan shi ne; mutum na iya yin tasiri wurin sauya dabi’un wasu mutane, amma a bangare guda kuma wannan mutumin babu yadda za a yi ya iya yin tasiri ga al’umma. Ko da a aikata ayyukan alheri ne, duk dagewarka, sai dai ka iya sauya dabi’ar kaso mai yawa, amma ba zai yiwu ka sauya komi da kowa, tsarin gudanarwa, da kuma cibiyoyi da bangarorin al’umma ba.
A lokuta da dama mutane na boye haqiqanin dabi’arsu don dai kawai su yi tasiri a zukatan wasu. A iya fahimtar masana halayyar jama’a da zamantakewa, don kawai ka ga mutum ya na yi maka murmushi, hakan ba ya na nufin murmushin qauna ko shauqi ba ne, wannan murmushin na buqatar fassara. Babu kuma yadda za a yi ka samu fassara wannan murmushi har sai ka yi mu’amala da wanda ya ke yi maka murmushin, sannan za ka san haqiqanin dalili.
Ta na iya yiwuwa me yin murmushin ya na so ne ya assasa wani tubalin abota a tsakaninka da shi, a wata mahangar kuma ta na iya yiwuwa me murmushin ya yi ne saboda ya shaidi fuskarka a wani wuri daban.
Matakin da za ka dauka bayan baquwar fuska ta yi maka murmushi ne zai samar da mafita ga murmushin. Misali idan bayan ya yi maka murmushi, sai kai ma ka mayar da murmushi, wannan zai isarwa da baqon fuskar saqon cewa ka aminta da murmushin da ya yi maka. Idan kuma mai neman a qulla abota ne, zai samu wata damar da zai gabatar da muradinshi.
Amma a dai dai lokacin da mutum ya ganka ya yi murmushi, sai ka murtuqe fuska, ko ma da me wannan me murmushin ya zo, zai samu cikas da sacewar gwiwa a yunqurinshi.
Ya na da kyau mu fahimci cewa a lokuta da dama idan mutum ya yi maka murmushi, ba ya na nufin murmushin farin ciki ba ne, wani murmushin na tashin hankali ne, wani murmushin na masifa ne, wani murmushin na mugunta da qeta ne. don haka fahimtar wanne irin murmushi ne baquwar fuska ta yi mana, dole ne mu natsu, mu fahimci a wanne yanayi ne a ka yi murmushin, shin ya dace da yanayin da za a yi murmushi ko a’a. ya fasalin me murmushin ya ke, shin ya yi kama da masu sakakkiyar fuskar da ta saba yin murmushi?
Sai na biyu, wurin da mu ke zaune (inda mu ke rayuwa) ya na da muhimmancin gaske ga dabi’unmu. Akwai wani bincike da wani masani mai suna Anderson ya gudanar a shekarar 1997, wanda bayan ya kammala ne ya fitar da natijar cewa, ‘Yanayin zafi na iya samar da dabi’ar mugunta, fushi, da zafin rai ga mutane’.
Abin da ya ke nufi shi ne wuraren da ke fama da matsanancin zafi na yanayi, wannan zafin na iya sawa a yi ta samun mutane masu dabi’u masu tsananin gaske.
Hatta wurin da mu ke zama, muhallinmu ya na taka muhimmiyar rawa a dabi’unmu. Ka kwatanta dabi’ar mutumin da ke kwana a cikin daki, na’urar bayar da iska na sanyaya shi, sannan akwai katifa da matashin kai mai laushi; da kuma mutumin da ke kwana a bakin bola, ruwan kwacami da kwadi na shagalinsu a gefenshi. Za ka samu hatta yanayin yadda wadannan mutane biyu ke tunani ya bambanta, haka kuma za ka ga dabi’unsu sun bambanta sosai. Dole dai shi makusancin bola ya ginu da dabi’ar son doyi, dauda da duk wani nau’insu.
Na uku, al’adunmu na da muhimmancin gaske a wurin gina dabi’ar dan Adam. Al’adarka a lokuta da dama ke gina ma dabi’ar qin wasu abubuwa, al’ada ke gina ma dabi’ar sanya tufafi nau’I kaza tare da gujewa nau’I kaza. Al’adarka ke gina maka dabi’ar qin aminta da abota da wasu nau’in mutane, tare da aminta da abotar wasu nau’in.
Daga qarshe, duk da akwai wasu abubuwa da daman gaske wadanda ke gina dabi’ar dan adam, amma zan so na taqaita ga yadda yanayin qirar halitta ke tasiri ga dabi’unmu.
Allah kan halicci mutane daban daban, wasu a yi su manya da babban jiki, wasu masu fadin qirji, wasu farare, wasu baqaqe. Wasu kyawawa wasu munana. Wasu sirara wasu masu qiba.
Babban misalin yadda qirar mutum ke tasiri ga dabi’armu shi ne; yadda a wasu yankunan qasar nan a ka samu ginuwar dabi’ar qwallafa rai ga farar mace. Yanayin yadda a ke son farar macen ma har ya baci, wannan ya sanya a ka samu sauyi a dabi’un musamman MATA a yanzu, ta yadda duk baqin mace sai kawai ta gina dabi’ar yin amfani da mai me sauya launin fata.
Wannan dabi’a ta amfani da me mai sauya launin fata ya ginu ne ya kuma tasirantu a zukatan mata sakamakon mayar da hankali da su ka ga maza su ke yi ga dole sai farar mace. Wannan wauta da rashin tunanin da wasu mazan kan yi dangane da wuce gona da iri wurin son farar mace, ya janyowa al’umma asara me yawan gaske, tare da haifar da wata dabi’ar tir ta sauya launin fata. Haka kuma aure sai ya zama ba a na bin diddigin tarbiyya da asali ba ne, saboda sun ce su na son ‘Fara ko aljana ce’. mu hadu mako mai zuwa.
DA GASKE MAZA SUN FI MATA SAURIN MUTUWA?
Tarihi ya tabbatar da cewa abubuwa uku ne ke tasiri a kan yawan mutane, bayan abubuwa ukun nan babu cikon na hudunsu. Na farko akwai mutuwa, akwai haihuwa sannan kuma hijira.
A wannan makon zan so ne mu shiga cikin mutuwa tare da fahimtar alaqarta da yawan al’umma (Population). Masana tun a farkon wannan fanni na ilmin sanin yawan al’umma ‘Demography’ sun fara yin bayanai ne dangane da mutuwa, bisa dalilin cewa ita mutuwa barazana ce ga yawan al’umma, ba ta qara yawan mutane, sai dai ta rage musu yawa.
Saboda wancan dalili ne masanan su ka ba al’amarin mutuwa muhimmancin gaske, su ka yi ta gudanar da binciken musamman domin a iya fahimtar MUTUWA da irin gudummawar da ta ke bayarwa ga ragewar al’umma.
Mutuwa dai dole ce, babu wata halitta da ta isa ta yi fariyan cewa ita da mutuwa sun raba gaari. Kowanne mutum ya na da alaqa da mutuwa, ko don wannan alaqar ta musamman da ke tsakanin mutane da mutuwa, ya ishi masana halayyar jama’a da zamantakewa su yi bincike a kanta.
Dukkanin mutuwa da kan auku su kan kasance daya daga cikin biyun nan; ko dai sanadiyyan gadon cuta daga Iyaye ko wata larura , na biyu ko kuma mutuwa sanadiyyan abubuwan da ke zagaye da mu na mu’amalar rayuwar yau da kullum.
Wannan ba taqaddama ba ne wanda a ka fara a yau, ko kwanakin nan ko kwanakin baya kadan. An tafka muhawara sosai dangane da wanda su ka fi saurin mutuwa tsakanin maza da mata a shekaru aru aru, wanda saboda a kaucewa zargin bin son rai, gudun kaucewa matakan tabbatar da ilmi ya sa masana su ka yi ta gudanar da bincike.
Ban manta ba, na taba karanta muhawarar wani masani mai suna John Grunt a binciken ilmin da ya gudanar a shekarar 1662 a Landan. Ya gudanar da binciken ne ta hanyar bibiyan dukkanin ofisoshin rijistar mutuwa inda ya tattara bayanai dangane da adadin yawan matattun da a ke da su. Sakamakon binciken John Grunt ya tabbatar da cewa ‘An fi haihuwar Maza fiye da Mata; sannan kuma Maza sun fi mata saurin mutuwa’.
Irin wadannan nazariyya su na nan da yawa wadanda masana su ka gudanar tare da fid da sakamako da dalilansu. A wannan sharhin nawa, kafa misali da binciken John Graunt kadai ya wadatar, saboda idan zan ci gaba da kawo misalai ba zan samu damar dora wasu bayanai masu muhimmanci ba.
A dai dai lokacin da a ka haifi jariri daga shekara 0, a wannan shekarar babban abun da ya fi komi sauqi shi ne ya kwashi qwayoyin cuta wadanda ke kashe garkuwan jikin dan Adam, saboda qwayoyin garkuwan jikin jariri ba su da qwari. Dalilin haka ne jarirai da dama ke kasa tsallake wannan shekara.
Ko a tsakanin shekara ta 0 da a ke tsammanin yawaitar mutuwan jarirai sakamakon iya diban qwayoyin cuta; Maza sun fi mata diban wadannan qwayoyin cuta, kuma sun fi mata mutuwa a lokacin da su ke Jarirai.
Dalilin da ya sa Maza su ka fi Mata fuskantar barazanar mutuwa a shekarar da su ke Jarirai shi ne; Mace Allah ya na halittarta ne da wasu kariya na musamman, wanda Namiji ba shi da su, wanda wadannan kariya na musamman da ke qumshe a jikinsu ne ke yi musu garkuwa da dukkan cututtukan da ke kashe garkuwan jiki.
Daga shekarar haihuwa sifili zuwa hudu, daga shekara hudu sannan garkuwan jikin jarirai ya samu kuzarin da ya kamata, don haka babu fargabar za su iya arba da qwayoyin cutan da ka – iya zama sanadiyyan rasa ransu.
Wani qarin matsalan na tasowa ne a lokacin da a ka cika shekara 15 a duniya, a wannan shekaran yawanci maza sun balaga, sun fara tunanin neman na kansu, saboda haka za su kutsa ga neman ayyukan da za su kafa kawunansu don dogaro da kai.
Saboda haka bayan nazari da binciken masana, lissafi ya tantance cewa daga shekara 15 zuwa sama Maza sun fi mata mutuwa, sannan sun fi Mata kasancewa a cikin hadurran da ka iya cinye rayukansu.
Dalili a nan shi ne, Maza su na fara ayyuka da sana’o’in da za su riqa barazana ga rayukansu, barazana ga garkuwan jikinsu, barazana ga dukkan wani tattali da su ke yi na kiwon lafiya. Irin wadannan ayyyuka sun hada da aiki a masana’antu, ma’adinai, masarrafa da sauransu. Misali, ya za ka kwatanta garkuwar jikin mutumin da ke aiki a ma’aikatar da a ke amfani da sinadarin ‘Chemicals’, wanda shaqarshi babban hadari ne ga rayuwa.
A wani bincike kwanan nan, wani bawan Allah mai sana’ar siyar da tabarma ya sanar da ni cewa; ya gano cewa dukkanin masu aiki a masarrafan tabarmu ba su jimawa su ke mutuwa, sakamakon sinadarin ‘Chemical’ din da su ke shaqa.
A nan akwai taqaddama babba, amma taqaddamar na tasowa ne kadai a Nijeriya da wasu qasashen da a ke kira da ‘qasashe masu habbaka’. Taqaddamar ita ce; a qasashen da su ka ci gaba babu barazanar mutuwa ga Mata masu juna biyu, saboda su na kiyaye duk wata qa’ida ta likitoci, sannan kuma akwai qwararru da asibitocin wadatattu.
Amma idan mutum ya kwatanta da irin qasarmu Nijeriya, zai ga cewa Mata sun fi rasa ransu a lokuta da dama yayin da su ke dauke da juna biyu. Don haka a nan za mu iya kawo cewa a shekara 15 zuwa 49 Mata a qasarmu su na fuskantar yiwuwar haduwa da mutuwa, saboda ba a basu kulawar da ta dace.
Daga shekara 49 zuwa sama, a wannan lokacin kuma garkuwan jiki ya fara yin sako – sako, don haka ko a sannan Maza sun fi mutuwa fiye da Mata, saboda har zuwa wannan lokacin kariyar musamman da su ke da ita daga Allah ba ta rabu da su ba.
Daga qarshe, zan so mai karatu ya san cewa wannan nazari ya ginu ne bisa tabbatattun hujjojin da a ke dasu, wadanda a ka samu bayan an gudanar da binciken ilmi ‘Research’ tare da kiyaye qa’idojin binciken. Mu hadu mako mai zuwa!
A wannan makon zan so ne mu shiga cikin mutuwa tare da fahimtar alaqarta da yawan al’umma (Population). Masana tun a farkon wannan fanni na ilmin sanin yawan al’umma ‘Demography’ sun fara yin bayanai ne dangane da mutuwa, bisa dalilin cewa ita mutuwa barazana ce ga yawan al’umma, ba ta qara yawan mutane, sai dai ta rage musu yawa.
Saboda wancan dalili ne masanan su ka ba al’amarin mutuwa muhimmancin gaske, su ka yi ta gudanar da binciken musamman domin a iya fahimtar MUTUWA da irin gudummawar da ta ke bayarwa ga ragewar al’umma.
Mutuwa dai dole ce, babu wata halitta da ta isa ta yi fariyan cewa ita da mutuwa sun raba gaari. Kowanne mutum ya na da alaqa da mutuwa, ko don wannan alaqar ta musamman da ke tsakanin mutane da mutuwa, ya ishi masana halayyar jama’a da zamantakewa su yi bincike a kanta.
Dukkanin mutuwa da kan auku su kan kasance daya daga cikin biyun nan; ko dai sanadiyyan gadon cuta daga Iyaye ko wata larura , na biyu ko kuma mutuwa sanadiyyan abubuwan da ke zagaye da mu na mu’amalar rayuwar yau da kullum.
Wannan ba taqaddama ba ne wanda a ka fara a yau, ko kwanakin nan ko kwanakin baya kadan. An tafka muhawara sosai dangane da wanda su ka fi saurin mutuwa tsakanin maza da mata a shekaru aru aru, wanda saboda a kaucewa zargin bin son rai, gudun kaucewa matakan tabbatar da ilmi ya sa masana su ka yi ta gudanar da bincike.
Ban manta ba, na taba karanta muhawarar wani masani mai suna John Grunt a binciken ilmin da ya gudanar a shekarar 1662 a Landan. Ya gudanar da binciken ne ta hanyar bibiyan dukkanin ofisoshin rijistar mutuwa inda ya tattara bayanai dangane da adadin yawan matattun da a ke da su. Sakamakon binciken John Grunt ya tabbatar da cewa ‘An fi haihuwar Maza fiye da Mata; sannan kuma Maza sun fi mata saurin mutuwa’.
Irin wadannan nazariyya su na nan da yawa wadanda masana su ka gudanar tare da fid da sakamako da dalilansu. A wannan sharhin nawa, kafa misali da binciken John Graunt kadai ya wadatar, saboda idan zan ci gaba da kawo misalai ba zan samu damar dora wasu bayanai masu muhimmanci ba.
A dai dai lokacin da a ka haifi jariri daga shekara 0, a wannan shekarar babban abun da ya fi komi sauqi shi ne ya kwashi qwayoyin cuta wadanda ke kashe garkuwan jikin dan Adam, saboda qwayoyin garkuwan jikin jariri ba su da qwari. Dalilin haka ne jarirai da dama ke kasa tsallake wannan shekara.
Ko a tsakanin shekara ta 0 da a ke tsammanin yawaitar mutuwan jarirai sakamakon iya diban qwayoyin cuta; Maza sun fi mata diban wadannan qwayoyin cuta, kuma sun fi mata mutuwa a lokacin da su ke Jarirai.
Dalilin da ya sa Maza su ka fi Mata fuskantar barazanar mutuwa a shekarar da su ke Jarirai shi ne; Mace Allah ya na halittarta ne da wasu kariya na musamman, wanda Namiji ba shi da su, wanda wadannan kariya na musamman da ke qumshe a jikinsu ne ke yi musu garkuwa da dukkan cututtukan da ke kashe garkuwan jiki.
Daga shekarar haihuwa sifili zuwa hudu, daga shekara hudu sannan garkuwan jikin jarirai ya samu kuzarin da ya kamata, don haka babu fargabar za su iya arba da qwayoyin cutan da ka – iya zama sanadiyyan rasa ransu.
Wani qarin matsalan na tasowa ne a lokacin da a ka cika shekara 15 a duniya, a wannan shekaran yawanci maza sun balaga, sun fara tunanin neman na kansu, saboda haka za su kutsa ga neman ayyukan da za su kafa kawunansu don dogaro da kai.
Saboda haka bayan nazari da binciken masana, lissafi ya tantance cewa daga shekara 15 zuwa sama Maza sun fi mata mutuwa, sannan sun fi Mata kasancewa a cikin hadurran da ka iya cinye rayukansu.
Dalili a nan shi ne, Maza su na fara ayyuka da sana’o’in da za su riqa barazana ga rayukansu, barazana ga garkuwan jikinsu, barazana ga dukkan wani tattali da su ke yi na kiwon lafiya. Irin wadannan ayyyuka sun hada da aiki a masana’antu, ma’adinai, masarrafa da sauransu. Misali, ya za ka kwatanta garkuwar jikin mutumin da ke aiki a ma’aikatar da a ke amfani da sinadarin ‘Chemicals’, wanda shaqarshi babban hadari ne ga rayuwa.
A wani bincike kwanan nan, wani bawan Allah mai sana’ar siyar da tabarma ya sanar da ni cewa; ya gano cewa dukkanin masu aiki a masarrafan tabarmu ba su jimawa su ke mutuwa, sakamakon sinadarin ‘Chemical’ din da su ke shaqa.
A nan akwai taqaddama babba, amma taqaddamar na tasowa ne kadai a Nijeriya da wasu qasashen da a ke kira da ‘qasashe masu habbaka’. Taqaddamar ita ce; a qasashen da su ka ci gaba babu barazanar mutuwa ga Mata masu juna biyu, saboda su na kiyaye duk wata qa’ida ta likitoci, sannan kuma akwai qwararru da asibitocin wadatattu.
Amma idan mutum ya kwatanta da irin qasarmu Nijeriya, zai ga cewa Mata sun fi rasa ransu a lokuta da dama yayin da su ke dauke da juna biyu. Don haka a nan za mu iya kawo cewa a shekara 15 zuwa 49 Mata a qasarmu su na fuskantar yiwuwar haduwa da mutuwa, saboda ba a basu kulawar da ta dace.
Daga shekara 49 zuwa sama, a wannan lokacin kuma garkuwan jiki ya fara yin sako – sako, don haka ko a sannan Maza sun fi mutuwa fiye da Mata, saboda har zuwa wannan lokacin kariyar musamman da su ke da ita daga Allah ba ta rabu da su ba.
Daga qarshe, zan so mai karatu ya san cewa wannan nazari ya ginu ne bisa tabbatattun hujjojin da a ke dasu, wadanda a ka samu bayan an gudanar da binciken ilmi ‘Research’ tare da kiyaye qa’idojin binciken. Mu hadu mako mai zuwa!
Uwa mai qarancin Shekaru: LABARIN ‘YAR SHEKARA 5 DA TA HAIHU
A wannan makon zan dan shiga cikin harkar haihuwa ne, saboda a makon da ya gabata mun tattauna batun mutuwa. Sai dai wannan zagayen ba zan yi bayanin haihuwa kaitsaye ta fuskacin alaqarta da qaruwar al’umma ba ne. Akwai labari mai muhimmancin gaske wanda shi ne zai dauki kaso mai yawa na rubutun.
Kamar yadda na fadi a gabatarwan rubutuna makon da ya gabata cewa ita mutuwa a ko da yaushe ta na janyo raguwan al’umma ne, sannan kuma ita mutuwa babu wanda zai ce shi babu ruwanshi da ita, ko da babu ruwanka da ita, ita akwai ruwanta da kai. Kowanne mutum dole ne ya na da alaqa da mutuwa.
Amma a al’amarin haihuwa kuwa, idan mutum ya ga dama babu ruwanshi da shiga sha’anin, saboda idan ka ga dama za ka iya qin yin aure, ko kuma ko da ma ka yi auren, sai ka dauki matakan hana samuwar haihuwa. Ka ga kenan, a bangaren haihuwa mutumya na da zabi biyu; ya haihu ko kar ya haihu. Wanda a al’amarin mutuwa babu wanda ke da wannan zabi, dole ne kawai a mutu.
A wasu lokutan ilmi na tabbatar da al’amarin da a ka shigar a kundi ne kawai. Kamar misali; za ka ga a na cewa wanda ya fi kowa dadewa a duniya shi ne dan shekaru 113, alhali ko kuma wataqil a qauyenku ma akwai tsohuwar da ta kai shekaru 120. Saboda ita tsohuwar da ke zaune a qauyenku lokacin da a ka haife ta babu wani rijistar haihuwa, wanda rashin wannan rijistar zai haifar da shakku gaa adadin shekarun da za ta fadi.
Idan Allah ya nufa, nan gaba kadan zan yi nazarin labarin matar da ta fi duk wata Mace yawan haihuwa a duniya, wata Mata ‘yar qasar Rasha, wacce ta haifi ‘ya ‘ya 69. Ka ga wannan labarin ya zama an amshe shi ne, saboda matakan da a ka bi wurin samunshi da tabbatar da sahihancin shi.
Haka kuma idan na ce ga labarin wata yarinya wacce ba a taba samun irinta a duniya ba; wacce ta haihu alhali shekarunta biyar da wata bakwai, ka ga zai yi wahala a samu wani wanda zai ce ai akwai wata, saboda wacce binciken musamman ya tabbatar ita ce dai wacce na ke magana. Idan kuma a ka samu wata a qauyenku ko garinku wacce ta haihuwa ta na shekaru 5 da wata shida shi kenan, ka ga an samu sabon ilmi da kuma sabon bayani kenan wanda ya shafe wanda a ke da shi a qasa.
A shekarun baya a 1939, wata ‘yar qaramar yarinya mai suna Lina Medina ta haifi jariri mai rai da lafiya, alhali shekarunta na haihuwa biyar da watanni bakwai. Wannan labara ya girgiza duniya, ya girgiza masana wadanda su ka tafi a kan cewa mace na fara al’ada ne daga shekara 15 zuwa 49.
Kamar yadda ya ke a ilmance, mace na iya daukan ciki (juna biyu) ne a lokacin da ta shiga shekarun da zai yiwu ta fara jinin al’ada, wanda a ke kira da ‘Menarche’ shi ne bincike ya tabbatar da shekara 15 a ke farawa, wannan na iya zama akwai bambanci a tsakanin qasashe. Sannan kuma wannan jini na al’ada na tsayawa a yayin da mace ta kai shekaru 49 ‘Menopause’ shi ma wannan akwai bambancin shekarun tsayawa a qasashe, saboda akwai matan da ke daukan ciki a shekaru 50 ko 51.
Dalilin da ya sa na kawo wannan misalin shi ne don a fahimci irin karya lagon binciken kimiyya da labarin yarinya Lina Medina ya yi; ba ma a shekaru 10 ko tar aba, a shekara biyar na yarinta ta dauki ciki, wanda hakan ke nuna ashe ta fara jinin al’ada ne tun a cikarta shekara biyar a duniya, ta haihu bayan wata bakwai.
Lina Medina ‘yar wani qauye ne da a ke kira Ticrapo da ke qasar Peru. A yayin da iyayenta su ka lura cikinta ya yi tulele, sai su ka yi zaton ko wani nau’in ciwo ne ya taru a cikinta wanda hakan ya sa su ka yi gaggawan kai ta garin Pisco domin a duba ta; bayan dogon binciken da likitoci su ka yi ne su ka tabbatar da cewa Lina na dauke da juna biyu na wata bakwai. Dakta Gerardo Lozada ne ya amshi haihuwanta kuma shi ne ya fara tabbatar da cewa yarinyar na da ciki.
Ganin haka ne fa a ka shiga yiwa iyayenta tambayoyin da a ke son jin amsoshinsu. Likita Gerardo a bincikensa ya gano cewa yarinya Lina ta fara jinin al’ada ne tun a watanni bakwai baya.
Wannan rikitaccen al’amari na buqatar gamsasshen bayani daga mahaifin Lina, wanda sanadiyyan haka ‘yan sanda su ka yi awon gaba da shi bisa zargin keta haddin diyarsa da kuma laifin fyade. Wanda dole ta sa daga baya a ka sake shi, saboda rashin bayyanannun hujjoji. An sanyawa jaririn suna Gerardo wanda nauyinsa ya kai kilo 2.7, wanda a kundin tantancewa ta zamo Uwa mafi qarancin shekaru. Jaririn da ta haifa mai suna Gerardo ya yi tsawon kwana a duniya, wanda sai da ya kai shekaru 40 kafin nan ya mutu.
Jaririn da Lina ta haifa har ya mutu bai san wanene haqiqanin mahaifinshi ba; shin Lina yayarshi ce (idan mahaifinta ne ke da cikin) ko kuma uwarshi? Lina Medina ta qi ta bayyana haqiqanin yadda a ka yi ta samu ciki.
Likitoci sun yi iyaka qoqarinsu wurin yin gwajin qwayoyin halitta domin tantancewa tsakanin mahaifin Lina da jaririn da ta haifa don samun tabbaci, amma hakan ya ci tura. Wannan labari ne ingantacce wanda ya auku, ba tatsuniya ba ne ko shaci – fadi. Mu hadu mako mai zuwa
Kamar yadda na fadi a gabatarwan rubutuna makon da ya gabata cewa ita mutuwa a ko da yaushe ta na janyo raguwan al’umma ne, sannan kuma ita mutuwa babu wanda zai ce shi babu ruwanshi da ita, ko da babu ruwanka da ita, ita akwai ruwanta da kai. Kowanne mutum dole ne ya na da alaqa da mutuwa.
Amma a al’amarin haihuwa kuwa, idan mutum ya ga dama babu ruwanshi da shiga sha’anin, saboda idan ka ga dama za ka iya qin yin aure, ko kuma ko da ma ka yi auren, sai ka dauki matakan hana samuwar haihuwa. Ka ga kenan, a bangaren haihuwa mutumya na da zabi biyu; ya haihu ko kar ya haihu. Wanda a al’amarin mutuwa babu wanda ke da wannan zabi, dole ne kawai a mutu.
A wasu lokutan ilmi na tabbatar da al’amarin da a ka shigar a kundi ne kawai. Kamar misali; za ka ga a na cewa wanda ya fi kowa dadewa a duniya shi ne dan shekaru 113, alhali ko kuma wataqil a qauyenku ma akwai tsohuwar da ta kai shekaru 120. Saboda ita tsohuwar da ke zaune a qauyenku lokacin da a ka haife ta babu wani rijistar haihuwa, wanda rashin wannan rijistar zai haifar da shakku gaa adadin shekarun da za ta fadi.
Idan Allah ya nufa, nan gaba kadan zan yi nazarin labarin matar da ta fi duk wata Mace yawan haihuwa a duniya, wata Mata ‘yar qasar Rasha, wacce ta haifi ‘ya ‘ya 69. Ka ga wannan labarin ya zama an amshe shi ne, saboda matakan da a ka bi wurin samunshi da tabbatar da sahihancin shi.
Haka kuma idan na ce ga labarin wata yarinya wacce ba a taba samun irinta a duniya ba; wacce ta haihu alhali shekarunta biyar da wata bakwai, ka ga zai yi wahala a samu wani wanda zai ce ai akwai wata, saboda wacce binciken musamman ya tabbatar ita ce dai wacce na ke magana. Idan kuma a ka samu wata a qauyenku ko garinku wacce ta haihuwa ta na shekaru 5 da wata shida shi kenan, ka ga an samu sabon ilmi da kuma sabon bayani kenan wanda ya shafe wanda a ke da shi a qasa.
A shekarun baya a 1939, wata ‘yar qaramar yarinya mai suna Lina Medina ta haifi jariri mai rai da lafiya, alhali shekarunta na haihuwa biyar da watanni bakwai. Wannan labara ya girgiza duniya, ya girgiza masana wadanda su ka tafi a kan cewa mace na fara al’ada ne daga shekara 15 zuwa 49.
Kamar yadda ya ke a ilmance, mace na iya daukan ciki (juna biyu) ne a lokacin da ta shiga shekarun da zai yiwu ta fara jinin al’ada, wanda a ke kira da ‘Menarche’ shi ne bincike ya tabbatar da shekara 15 a ke farawa, wannan na iya zama akwai bambanci a tsakanin qasashe. Sannan kuma wannan jini na al’ada na tsayawa a yayin da mace ta kai shekaru 49 ‘Menopause’ shi ma wannan akwai bambancin shekarun tsayawa a qasashe, saboda akwai matan da ke daukan ciki a shekaru 50 ko 51.
Dalilin da ya sa na kawo wannan misalin shi ne don a fahimci irin karya lagon binciken kimiyya da labarin yarinya Lina Medina ya yi; ba ma a shekaru 10 ko tar aba, a shekara biyar na yarinta ta dauki ciki, wanda hakan ke nuna ashe ta fara jinin al’ada ne tun a cikarta shekara biyar a duniya, ta haihu bayan wata bakwai.
Lina Medina ‘yar wani qauye ne da a ke kira Ticrapo da ke qasar Peru. A yayin da iyayenta su ka lura cikinta ya yi tulele, sai su ka yi zaton ko wani nau’in ciwo ne ya taru a cikinta wanda hakan ya sa su ka yi gaggawan kai ta garin Pisco domin a duba ta; bayan dogon binciken da likitoci su ka yi ne su ka tabbatar da cewa Lina na dauke da juna biyu na wata bakwai. Dakta Gerardo Lozada ne ya amshi haihuwanta kuma shi ne ya fara tabbatar da cewa yarinyar na da ciki.
Ganin haka ne fa a ka shiga yiwa iyayenta tambayoyin da a ke son jin amsoshinsu. Likita Gerardo a bincikensa ya gano cewa yarinya Lina ta fara jinin al’ada ne tun a watanni bakwai baya.
Wannan rikitaccen al’amari na buqatar gamsasshen bayani daga mahaifin Lina, wanda sanadiyyan haka ‘yan sanda su ka yi awon gaba da shi bisa zargin keta haddin diyarsa da kuma laifin fyade. Wanda dole ta sa daga baya a ka sake shi, saboda rashin bayyanannun hujjoji. An sanyawa jaririn suna Gerardo wanda nauyinsa ya kai kilo 2.7, wanda a kundin tantancewa ta zamo Uwa mafi qarancin shekaru. Jaririn da ta haifa mai suna Gerardo ya yi tsawon kwana a duniya, wanda sai da ya kai shekaru 40 kafin nan ya mutu.
Jaririn da Lina ta haifa har ya mutu bai san wanene haqiqanin mahaifinshi ba; shin Lina yayarshi ce (idan mahaifinta ne ke da cikin) ko kuma uwarshi? Lina Medina ta qi ta bayyana haqiqanin yadda a ka yi ta samu ciki.
Likitoci sun yi iyaka qoqarinsu wurin yin gwajin qwayoyin halitta domin tantancewa tsakanin mahaifin Lina da jaririn da ta haifa don samun tabbaci, amma hakan ya ci tura. Wannan labari ne ingantacce wanda ya auku, ba tatsuniya ba ne ko shaci – fadi. Mu hadu mako mai zuwa
Saturday, 11 April 2015
Nazarin Kalmar 'SO'
Na
karu matuka a makon da ya gabata yayin da na ke sauraron Farfesa Peter Kreeft,
wani farfesan falsafa a kwalejin Boston.
Farfesan
hazikin masani ne wanda ya ke bayani dai dai gwargwadon fahimtar daliban
Falsafa, har ma da sauran masu neman haske.
Ya
yi jawabi ne a Ikhlisiyyar (Coci) wani gari dangane da 'Soyayya wacce Allah ke
kimtsawa zukata', daga farko har karshen jawabin Farfesa Kreeft ya yi ta kafa
hujjojin hankali ne dangane da 'Soyayya'. Ya kuma bambance tsakanin 'Soyayyar
da Allah ya kimtsa a zukata', da 'Soyayyar da mutum ya cusa ma kanshi'. Dalilin
wannan nazari na Bafalsafe Kreeft ne na tsunduma tunani mai zurfi dangane da
Soyayya.
Abun
damuwa shi ne yadda a ke sarrafa kalmar 'SO' a wannan zamani na mu. Idan za ka
bi mutane daya bayan daya ka na yi musu tambaya dangane da Soyayya, za a ba ka
hadin kai wurin amsa tambayoyin amma fa za ka tarad da amsoshi masu sarkakiya.
Ka
natsu da kyau, sai ka yi nazarin kalamai irinsu "Ina sonki",
"Ina son matata", "Ina son Mota ta", "Ina son
Barcelona", "Ina son Alewa", da kuma "Na tsunduma a cikin
soyayya". Dukkanin wadannan kalamai su na iya daidaita wurin furuci amma
kuma ba dole ma'ana ta zo daya ba. "Soyayya" wani fanni ne na rayuwar
yau da kullum. Wasu na rasa rayuwarsu sanadiyyar So, wasu kuma na yin rayuwar
din din din ne a cikinshi.
Gabakidaya
kamfanonin wallafa na mawaka da masu hada katin soyayya da gaisuwa, su na cin
riba ne sakamakon wanzuwar Soyayya.
Dattijon
masanin falsafan nan, Aristotle ya zayyana salon soyayya a cikin falsafarshi
ta 'Nicomachean Ethics'. Babban mahangar littafin da alkiblarshi
shi ne kokarin fassara ma'anar 'Farin ciki'.
Aristotle
ya ce "Idan a na batun soyayya, toh sai mutum ya na son kanshi kafin ya
iya son wani." Watakila wasu, su ga ba haka ba ne. {ila ma wani ya ce Son
rai Aristotle ke koyar da mutane.
Abun
lura a nan shi ne, ba wai son rai fa Aristotle ke magana a kai ba. A'a, mutum
ya san darajar kanshi ta hanyar kula da taka tsan-tsan ta haka zai iya kiyaye
daraja da matsayin sauran mutane.
Saboda
dai Bafalsafe Aristotle ya wanke kanshi daga zargi, sai ya ci gaba da cewa matukar
‘son kai’ zai sa mutum ya tattara dimbin dukiya ya kuma yi danniyan mulki har
ta kai ya cutar da mutane, to ba irin wannan a ke nufi ba.
A
tsakanin masana falsafa ma akwai wata Baturiya mai suna Ayn Rand wacce ta
bayyana ra’ayinta dangane da ‘Soyayya’. Ita dalibar falsafan ‘Individualism’
ce ba fannin makarantar Aristotle ba. a wani tattaunawa da a ka yi da ita a
shekarar 1964, ga abun da ta ce dangane da soyayya: ‘Soyayya ba dole sai mutum
ya fara da son kanshi ba tukunna, wani abu ne wanda ko hanya bai hada da wannan
ba. Idan akwai wani wanda ka ke so, to lallai za ka muhimmanta wannan wanda ka
ke so din, sannan kuma soyayyarshi na iya tasirantuwa akanka ka canza’.
Yanzu
misali, ka na tafiya a titi lafiya kalau, sai kawai kwatsam wata budurwa ta
fito daga wani shago, kawai sai ka kamu da sonta a ganin farko!, Me ke janyo
irin haka?.
Amsar
a bayyane ta ke, ya danganta da yadda zuciyarka ta ke aiki. Idan da ma ka na
zaman kadaici ne, to zuciyarka za ta kasance a bude wurin neman wacce za ta
cike ma gurbi. Duk kuwa taka tsan-tsan din mutum da dauke kanshi, wajibi ne
watan watarana sai zuciyarshi ta yi kicibis.
Na
san da yawan mutane, musamman a kasar hausa sun yi imanin cewa soyayyar da a ka
fara ta farad daya ba ta daurewa, alhali kuma ba haka abun ya ke ba. sai dai
samun irin hakan ya na da dan wahala.
Za
ka iya haduwa da wani, ka fara sonshi farad daya saboda wannan tanadi na zuciya
dangane da irin wanda za ta yi soyayya da shi. Ta ya ya hakan zai yiwu, alhali
ba ka taba yin magana da shi ba?. Eh, domin zai yiwu cikin tanadin zuciyarka
akwai salon tafiya, fasalin magana, kallo da sarrafa idanu. Dadin dadawa kuma
ma wannan na iya faruwa cikin sauki idan wacce ka gani din ta tuna ma ka wata
masoyiyarka.
Ya
na da kyau mu fahimci cewa, duk wanda tanadin zuciyarshi ya fi karkata zuwa ga
ado da kyawun fuska fiye da sauran muhimmin abubuwa, zai fi kowa saurin fadawa
soyayya a ganin farko.
Kowanne
dan Adam ya na da irin tsarin rayuwa, tsarin da ke wanzuwa a cikin zuciya.
Yanayin tasowar mutum, yarinta da muhallin da ya taso na iya yin tasiri a kan
irin abokin soyayyan da zuciyarshi ke so.
Zan
kawo misalin yadda wani Mukhtar (wanda na tattauna da shi) ke son abokiyar
soyayyarshi ta kasance;
1. Ya zama iliminta ya zo daya da na shi, ko ba
ta kai shi ba, ta kusa cimmai a fagen ilmi
2. Kar ta kasance mai yawan
surutu (saboda Mukhtar ya camfa cewa yawancin mata masu surutu, soyayya da su
bai haifar da da mai ido).
3. Ta kasance ta iya
mu’amala da mutane (Saboda Mukhtar bai iya mu’amala da mutane ba sosai, kuma ya
ji labarin ance abokin soyayya na tasiri akan dan uwanshi).
Duk
wannan dogon bayani da na ke ta faman zayyanowa ina so ne na bayyana
muhimmancin soyayya da kuma yadda ta ke da tasiri a zukatan ‘yan Adam. Za ka ga
na wani ya fi na wani. Wasu ma sai ka yi zaton gabakidaya rayuwarsu babu abun
da su ka iya sai soyayya. Wani kuma namiji ne amma da zaran ya ga mata sai ya
fara sunkuyar da kai, saboda ya na tsoron ma su hada ido.
Tuntuni
na ke tunanin wai me ya sa a ka damu da soyayya ne?, ba zan fadi ko ‘A’ ba, kai
ma ina so ne ka tsunduma cikin tunani ka gano me ya sa?.
Mu
hadu mako mai zuwa.
Subscribe to:
Posts (Atom)