Lallai sauyi ya zo; wata rana ina zaune a kofar gida,
na jima ban ji almajiri na bara ba (neman taimakon abinci), bayan sallar Isha’i
ne. kawai sai na ji wani ya zo, abun da ya bani mamaki shi ne sai da ya yi sallama.
Ni a baya ban san almajirai na sallama ba kafin su fara bara.
Ya ce;
“Assalamu Alaikum, wahidi iya, sabida Allah, a taimaki almajiri Iya, domin
Allah, don Kur’ani, ko dan kanzo, ko gaya ne ba miya Iya, Iya yunwa ba ta da
hankali.”
Har
abada duniya ba za ta manta da tarihin
siyasar Nijeriya ba, musamman a zamanin dimokradiyya wacce ta faro daga
shekarar 1999 bayan gushewar mulkin Soja sakamakon faduwar gwamnatin Janar Sani
Abacha ta hanyar mutuwa.
A
lokacin sai wadanda a ke gani a matsayin jiga jigai a dukkan fannoni na
Nijeriya, su ka kirkiri jam’iyyar PDP, wacce ita ta fara mulkin farar hula na
dimokradiyya, bayan zagayowar shekaru hudu cur, a shekarar 2003 jam’iyyar ta ci
gaba daga inda ta tsaya, wasu shekaru hudun su ka zo, a shekarar 2007 jam’iyyar
PDP din ne dai. Bayan an lashe wasu shekaru hudun, a shekarar 2011 labarin dai
shi ne babu wani canji, PDP.
Wannan
tagomashi da nasara, da karfi da izza da jam’iyyar PDP ke ganin ta samu, wanda
a hakikanin gaskiya akwai karfin, kuma wannan karfi ya tsole ma ‘yan Nijeriya
ido, karfin ya takurawa ‘yan Nijeriya musamman talakawa.
Hatta
jiga jigai, wasu ma da su a ka kafa jam’iyyar PDP idan masu mulki ko uwa a
bakin murhu su ka yi wani siddabarun wanda ya saba da hankalinsu, ba su isa su
ce uffan ba; ko dai su yi shiru ko kuma su yi magana a tsangwame su, idan ma ba
su yi sa’a ba, sai a yi amfani da wannan karfi a toshe su, a kashe kaifin
tasirinsu.
Wannan
karfi na jam’iyyar PDP ya sa a yawancin lokuta a ke kiranta da giwar jam’iyya a
nahiyar Afrika. Duk wani abu da jam’iyyar PDP ta sa a gaba, zaman lafiya da
kwanciyar hankalin kowa shi ne ta kai ga nasara, saboda idan ba haka ba, kowa
zai ji a jikinsa.
Hatta
al’amarin da ya auku a shekarar 2011 na kone konen muhallan ‘yan jam’iyyar PDP
a Arewa, sakamakon zargin murda murda a wasu jihohi. Maimakon ya nuna karshen
kaskanci ga jam’iyyar, sai dai ma ya zama hannun jari ga ‘ya yan jam’iyyar da a
ka kone ma gidaje da dukiyoyi. Idan an kona maka gida, uwar jam’iyyar za ta
mayar maka da wani sabon gida a unguwar da ta fi na ka, da kayan bukatun rayuwa
cike da gidan, sannan ta gyara maka gidanka fiye da baya.
Idan
dukiya a ka lahanta ma, za su mayar ma da ninkinta ba tare da dar dar ko
faduwar gaba ba. Irin wannan nuna karfi da isa na jam’iyyar PDP ne ya kwantar
da hankalin ‘ya ‘yan jam’iyyar, har su ke ganin shekaru 60 da su ke mafarkin za
su yi su na mulkar Nijeriya, babu makawa sai sun kai cur sannan za su takawa
tafiyar burki (shi ma idan sun so).
‘Ya
‘yan jam’iyyar PDP, musamman manyan jam’iyya sun dau wani irin girman kai da
dagawa sun jibgawa kawunansu. Wannan zakin karfin jam’iyyar PDP ne ya yaudari
mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo ya ke cewa babu wasu dattawa a Arewa sai
shi. Shi a iya ka tunaninsa dattijontaka shi ne karfin ikon taka duk wanda ka
so, tare da juya duk abun da ka so.
Shi
bai san cewa dattijo, natsattse ba ne, kammalalle wanda ya san ya kamata, ya ke
kiyaye hakkokin wadanda Allah ya ba shi aron karfi a kansu, ba wai ya yi amfani
da karfin wurin danne duk wanda ya nuna mishi yatsa ba.
Wannan
zakin karfin jam’iyyar PDP ne ya sa mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo duk
ranar da zai shiga Kaduna a karshen mako, mutane da yawan gaske su kan rasa
kasuwancinsu, saboda jami’an tsaro na tarwatsa duk wata hidima da ta shafi
hanyar da zai bi. Maimakon a matsayinshi na mai ikirarin dattijo ya kiyaye irin
wannan.
Wani
babban abun mamaki shi ne irin nuna isa da karfin iko da matar shugaban kasar
Nijeriya , Madam Dame Patience Jonathan, wacce a kafafen watsa labaru a ke yi
mata lakabi da ‘Mama Peace’ wai maman zaman lafiya.
Ka na
kallon fuskan Mama Dame Patience ba ka bukatar a ce ma ka irin mutanen nan ne
da ke sako magana ba dadin ji. Tun bayan da Allah ya dauki rayuwar marigayi
Umaru Musa ‘Yar’aduwa, mataimakinshi shugaba Goodluck Ebele Jonathan ya maye
kujerar, Mama Patience ta fara zubo maganganu, har ta kai ‘yan kasa na
tsokanarta, musamman a fannin gurbataccen turanci da ta kware a kansa.
Lokacin
da babban zabe ya matso a shekarar 2015, Mama Patience ta yi ta sakin layi, sai
dai abun bai wuce gona da iri ba, har sai bayan da a ka dage zaben shugaban
kasa zuwa 28 ga watan Maris, daga nan ne fa ta karbi ragamar yakin nemawa
mijinta dawwama a kujerarsa.
Duk
inda ta je yawon kamfen sai ta kafa tarihi, bakin tarihi ga Nijeriya da bakin
fenti ga matsayin uwargidan Shugaban kasa. Wani wurin ta ce ai Janar Buhari
kwakwalwarshi ta zama jabu, ta kusa daina aiki. Me za a ci da mutum tsofai –
tsofai, zai zo ya na takara da ‘ya ‘yan cikinshi. A jihar Ribas cewa ta yi, duk
wanda ya zo ya ce musu chanji, su yi mishi jifan rajamu ba kakkautawa.
Mafi
munin sakin bakin ‘Mama Peace’ shi ne inda ta ke cewa wai mai gidanta bai
bukatar kuri’un ‘yan Arewa. Mutanen da ba su da aiki sai haihuwar yara su na
zubarwa a titi, karshe su zama Almajirai.
Lallai
fa MAMA kin ga aikin almajirai. Su ne dai su ka yi ruwan miliyoyin kuri’u daga
jihohin Kano, Katsina. Mama almajiran jihar Kaduna, Yobe, Sakkwato da Zamfara
duk sun ki su zabi mijinki. Almajiran jihar Adamawa, da na jihar Kebbi duk sun
ki jefa ma mijinki ne saboda kin ce a kai kuri’unsu kasuwa. Mama almajiran
jihar Borno sun jima cikin kuncin kisan gilla, dole ta sa su ka ce, su dai PDP
Sam!
Mama
Patience baki shi ke yanka wuya; maimakon ki ja bakinki ki yi shiru, ga shi
yanzu kin janyowa mijinki asarar kuri’un dukkan almajiran Arewa, ‘ya ‘yan da
kika yiwa kazafin a na banzantar da su a titi.
Cikin
fushi da hasala da irin wadannan kalamai na ki marasa fasali da dadin ji,
almajiran nan su ka yi mursisi, su ka yi ta ruwan kuri’u ga babban almajiri,
mutumin da ki ka kira da tsofai tsofai, wanda ki ka ce kwakwalwarsa ta mace;
shi din dai, da wannan kwakwalwa ya yi tasiri a kan mutanen yankin Yarbawa.
Mama ya ki ka ga aikin mutanen Osun, Oyo, Legas? Mama mutanen Binuwai ma sun
fusata, watakila su ma almajiran ne, domin babban almajiri Janar Buhari tsaf ya
cinye jihar.
Mama
na san sarai kin kasance a gaban akwatun talabijin dinki, a dai dai lokacin da
dattijon yankinku na Neja Delta, Orubebe ya tayar da hayaniya a dai dai lokacin
da a ke tattara sakamakon alkaluman jihohi. Shi dole tsagera, amma abun mamaki,
ko da ya gama kumfar baki da cije cije hade da zare idanu, sai almajiri Jega ya
nuna mishi irin dattijontakan almajiran Arewa, ya kwabe shi, ya yi mishi
nasihar da duk duniya sai da a ka jinjinawa wannan salo na Farfesa Attahiru
Jega. A cikin ruwan sanyi, ya tsula ma mai kiriniya tsumagiya, ya dawo
hayyacinshi.
Mama
ya kamata ki sani har abada mutanen yankin Neja Delta da ‘yan uwan shugaba
Goodluck Jonathan, da jikoki da tattaba kunne, har ma da ‘ya ‘yan jam’iyyar PDP
ba za su taba mantawa da wannan mummunan kaye da sakakkun kalamanki su ka janyo
musu ba. Yanzu lokaci ne da ya dace ki bi gida gida na ‘yan jam’iyyar PDP masu
mafarkin shekara 60 su na mulki, ki basu hakurin harzuka almajirai da ki ka yi
su ka kifar da jam’iyyar da ruwan kuri’u. WAHIDI
IYA! Mu hadu mako mai zuwa
No comments:
Post a Comment