Duk
wata qasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan ka waiwaiyi sirrin da ke tattare
da samuwar wannan ci gaba, za ka ga a hannun matasansu ya ke. Saboda basu yin
sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa.
Haqqi
ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye da su kasance mataki na farko a inda ‘ya
‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin qasa da oda,
kaucewa ayyukan barna da sauransu.
Idan
iyaye su ka gaza aikata hakan ga ‘ya ‘yansu, babu tantama a dai dai lokacin da
yaron ya kai shekarun girma (Matashi) ya fara mu’amala da wasu abokai a waje za
su koya mishi dukkan dabi’un da su ka ga dama. A wasu lokutanma ba sai sun koya
mishi ba, yanayin mu’amala a tsakaninshi da su ne zai sa ya riqa kwaikwaiyon
yadda su ke tafiyar da rayuwarsu a hankali har ya gina dabi’a.
Wannan
ya nuna cewa haqqin iyaye ne, kuma ikon kiyaye ‘ya ‘ya daga fadawa hadurran
kwaikwayon halayen banza a waje na hannun iyayen ne. wanda idan a ka samu kaso
60% cikin 100% su na sauke wannan nauyi, za a ga chanji.
Qasashen
da su ka ci gaba din nan, doka ce mai qarfi wacce ta tilasta iyaye a kan
tarbiyyar ‘ya ‘yansu. Har ma idan iyayen ba su iya yi ba, sai hukuma ta dauki
wannan babban aiki, saboda fahimtar irin hadarin da ke tattare da barin matasa
cikin halin rashin bambance kyakkyawa da mummuna.
A qasashen
Afrika, sai ya kasance kaso mai yawa na iyaye babu ruwansu da halin da ‘ya
‘yansu za su shiga idan har basu dauki nauyin kula da tarbiyyarsu ba. Haka kuma
a wannan yanki namu na Afrika, iyaye da dama (sai dai kadan) ba su wani
taka rawar a zo a gani wurin hobbasa kan
‘ya ‘yansu su yi karatu.
Halayen
banza da aikata duk wani aiki da zai cutar da mutum ko ya janyo asarar dukiya
ya na da alaqa da jahilci. Saboda shi jahilci babu abun da ya ke umurtar qwaqwalwa
ta aikata face son rai da aiki ba tare da tantancewa tsakanin mai kyau da marar
kyau ba.
Wannan
shi ne dalilin da ya sa baragurbin ‘yan siyasa, wadanda ba burinsu ganin ci
gaban Nijeriya ba, su ke amfani da matasa wurin cimma mummunar manufarsu ta
aika aika. Su ne su ke ba matasan makamai da qwayoyi.
Daya
daga cikin abun da ke tashe a tsakankanin matasa a Nijeriya shi ne bangar
siyasa da rikici. Wannan al’amari ya na da matuqar hadarin da idan ba an
magance shi ba ne, lallai ba zai taba yiwuwa a mori dimokradiyya ko wanzajjen
zaman lafiya ba.
A
al’ummun da su ka ci gaba ba qaramin aibu bane a kira mutum da dan bangar
siyasa ballantana kuma daya daga cikin masu hura wutar rikicin siyasa, amma a
Nijeriya wannan ba komi ba ne. Wannan bangar siyasa ta bambanta da asalin ‘yan
sara – suka da mu ke da su, da ‘yan kalare da ‘yan daba.
Duk
inda a ka kira wadancan sunaye, musamman a garuruwan Bauchi, Kano da Gombe,
suna ne wanda ya shafi matasa masu ayyukan rashin mutunci, rashin da’a da keta
haqqoqin al’umma.
Zaben
shekarar 1999, wanda tsohon janar, Olusegun Obasanjo ya lashe. Sai dai tun a
wannan lokaci ne ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan rikicin zabe da bangar
siyasa a tsakankanin matasa. Wannan irin mummunan dabi’a ta ci gaba da faruwa
har a zaben shekarar 2003 da a ka yi. Maimakon a samu sauqe sai dai ma a ka yi
ta samun qaruwar dabi’ar bangar siyasa da rikicin zabe ga matasa.
‘Yan
siyasa masu mugun nufi a lokuta da dama su na aiki da matasan ne wurin sace
akwatunan zabe, kai farmaki, da qone - qonen da su ka sabawa shari’a.
Yanayin
da ke fuskantarmu, bisa la’akari da
gabatowar babban zaben shekarar 2015, alamu na nuna matasan da ba su da ruwa da
tsaki da da kalare, daba ko sara – suka akwai yiwuwar su fada ma irin wannan
mummunan aiki na bangar siyasa da rikicin zabe.
A
lokacin da a ka yi zaben fid da gwani na jam’iyyu a Nijeriya, an samu rahotannin
yadda wasu ‘yan siyasa a jam’iyyun su ka yi amfani da matasa wurin tayar da
hankula domin kawai su yi qaurin suna.
Ya
kamata ne matasanmu su hankalta, su gane cewa bangar siyasa da rikicin zabe
babu wani alheri da su ke haifarwa, sai dai sharruka birjik.
Rahotanni
sun adana cewa a rikicin zaben shugaban qasa da ya auku a watan Afrilun 2011 ya
yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 800, kamar yadda hukumar kare haqqin
bil’adama su ka bayyana. Wadanda su ka mutu din an kashe su ne cikin kwanaki
uku a jihohin arewa 11, wanda a kasha 90 na kashe – kashen matasa ne su ka
aikata, haka ma rikicin zaben matasa ne su ka tayar.
Zaben
shekarar 2011 da ya gabata ya tafi ya bar baya ta qura, bilhasali ma ba a taba
yin zabe wanda a ka zubar da jinni kamar shi ba. An tarwatsa mutane daga
muhallinsu, wasu sun rasa iyaye da ‘yan uwa. Hukumar bayar da tallafin gaggawa
ta shaida cewa sama da mutane dubu 65,000 ne su ka bar gidajensu sakamakon
rikicin.
Idan
matasa su ka hankalta ta hanyar qauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas
baragurbin ‘yan siyasa da basu son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga
cimma burinsu ban a zubar jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
A
matsayinka na matashi, ya kamata ne ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina
rayuwarka, a samar da ayyukan da matasa za su yi bankwana da zaman banza, a
samar musu guraben karatu a makarantun da mu ke da su; wannan shi ne aikin gina
rayuwar mutum ba a bashi makami da qwaya ba. Makami da qwaya sai dai rusa
rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da ka ke tare da
su. Mu
hadu mako mai zuwa!
No comments:
Post a Comment