Saturday, 17 January 2015

Bankwana da zaman lafiya: Kirkirarrun masifu, da bala'o'i

 
Nijeriya kasa ce mai muhimmancin gaske, wacce hatta kasashen duniya da a ke ambato da tinkahon duniya 'super powers', su na kiyayewa da mutunta wannan matsayi.
Wannan matsayi da Nijeriyarmu ta samu, ya samo asali ne daga wasu daidaikun abubuwa da su ka hada da yalwataccen tattalin arziki; girman kasa mai albarkatu. Da kuma yawan adadin mutane wadanda alkalumma ke tabbatar da cewa sun kai miliyan 150 (tun muna yara ake wannan hasashe).
Akwai yaduwar mutane a dukkanin kusurwowin kasar, Arewaci sun fi kowa yawa, akwai a kudanci, Yammaci, da Gabashi.
Shekaru kadan baya rigingimu su ka fara yi wa yankin Arewacin Nijeriya zaizaiya ta kasa, a hankali tun ba a ankara ba, har ta kai a yau, an ankare.
Sauyin yanayi ya kawo mu wani zamani na rainin hankali, wanda karfin iko da mulki ba su tafiya dai dai har sai an sirka su da dabarun mallakar kwakwale da tunanin al’umma.
Kuma zamani wanda a ke haifar da bala’i, masifa, tashin hankali, barazana, firgici domin samar da mafita ga wata matsala.
Tun shekaru aru aru wasu kasashen duniya su ke amfani da irin wannan lissafi domin cimma burinsu.
Wannan bahaguwar falsafa ba ta samu wurin zama na musamman a Nijeirya ba, har sai wannan lokaci na mulkin farar hula wanda ke tafiya bisa turbar dimokradiyya. Tun mutane ba su fahimta, har ta kai a na fahimtar sabon salon, kuma kowanne shugaba idan ya zo, ya na zuwa ne da irin na shi rainin hankalin.
Wannan dabara da wasa da hankali ne ya samar da mutane irinsu Alhaji Muhammad Dokubo Asari, wanda a ka kirkire shi a cikin dirkirarrun tsagerun yankin masu gadara da shimfidadden danyen man fetur a karkashin kasa (Neja Delta).
Ga wadanda sunanshi kawai su ke ji, Dokubo Asari mutum ne wanda bai iya furuci ba ko miskala, hotunanshi babu abun da su ke siffantawa face rashin natsuwa da kamala.
Mayaki ne (a ikirari) wanda bai san salo da dabarun fito na fito ba, shugaba ne (na ‘yan tsagera) wanda wakilcin shi ga wadanda ya ke wakilta abun tir ne da Allah wadai.
A wannan makon na sadaukar da wannan shafi ne don wayar da kawunan wadanda a ke son a zurma su cikin rami kuma a rufe.
Samuwar Arewa da rashin samuwarta ya na a hannun al’umman yankin ne, idan sakaci da rashin sanin ya kamata ya sa su ka lankwashe hannuwa, su ka rungumi kaddara (kamar yadda kakanninsu su ka yi a ka yage Nijar daga Arewa), ai kuwa dole ne ta fashe a yi wasosonta.
Barazanar ‘ya ‘yan biyuu-ahu irinsu Dokubo ba shi ne babban matsalar ba, su dai kumfar bakinsu kamar ‘yar nune ce wacce ke shaidawa al’umman yankin cewa sha-zumamu na sunsuno zaki.
Mutum mai iyali, wanda shi ne shugaban gidanshi ba zai kuskura ya fadi wata magana wacce furta ta zai iya tarwatsa zaman lafiyan gidan ba. kai ko da kuwa rashin zaman lafiyan tsakanin gidanshi da gidajen makwabta ne.
Ballantana kuma a ce shugaba, ba abin mamaki ba ne ga shugabannin yankin Neja Delta, tunda ba farau ba inda sakin layi ne a fadi zancen bur. Sai dai kalaman Alhaji Dokubo dole ne a daura a sikili a yi nazarinsu.
Ga kadan daga cikin irin zantukanshi wanda na nakalto kaitsaye daga jaridar Vanguard ta ranar 11 ga watan Mayun 2013. “Ina son jaddada cewa babu fa zaman lafiya da zai wanzu, ba wai a yankin Neja Delta ba, a’a a dukkanin Nijeriya, matukar Goodluck Jonathan bai ci zaben 2015. Sai dai idan kuwa Allah ya dauke rayuwarshi ne, wanda kuma ba mu fatan haka. Kamar yadda tsarin mulki ya zo da shi, Jonathan ya na da shekaru 8 cur wadanda zai yi a kujerarshi.”
A wasu yankunan, idan ka ji mutum na fadin irin wadannan soki – burutsu za ka ji a na cewa ya na yin zancen ‘yan tasha. Domin a tasha ne za ka je ka tarar da zauna gari banza, marasa ta ido. Hatta ‘yan tashan cikin siyasa daidaiku ne za su iya runtse ido su yi ta soko maganganu haka.
Sai dai kash!, mutumin fa da ya ke ta wadannan maganganu ba komin komai ba ne, kuma ba kowa ba ne shi, zaman lafiya kuma da ya keta kurarin zai kare ai mu tuni a yankin Arewacin Nijeriya mu ka yi bankwana da zaman lafiya. Manyan jihohinmu da mu ke takama da su kirkirarrun tsagera takwarorin su Dokubo sun tarwatsa ma na su da bama bamai.
Sai da a ka tarwatsa zaman lafiya a shahararren birnin Jos, wanda kafin rikici a ke wa lakabi da gidan zaman lafiya. Irin wannan kirkirarren rikicin addini da kabilanci ne kuma a ka haifar a jihohin kaduna da sauransu.
Rikicin addinai da kabilanci ya biyawa wadanda su ka kirkiro shi bukata. Haka nan kuma rikicin tsageran Neja Delta ma ya biyawa kirkirarrun tsagera bukata ta samun makudan kudade.
Ga kirkirarriyar gwagwarmayar nan ta Boko Haram wacce a ke amfani da sunanta a na ruguza jihohin Yobe, Maiduguri, Kano, Kaduna, da wasu jihohin Arewa.
An yi amfani da sunan Boko Haram din an jibge sojoji a cikin gari su na ta yiwa mata fyade, su na wulakanta mutanen da ba su ji sun gani ba. An kafa shingen sojoji a kowanne sako da lungu. A irin wannan hali, idan mu ka yi shiru, mun ci amanar alkalami, baiwa da hikimar Allah.
Wannan shi ne yanayi mafi tashin hankali, shi ne yanayi na firgici, shi ne yanayi na zulumi da fargaba.
Masifu sun mamaye mu, sun yi mana kawanya, duk dai don a cimma wata boyayyiyar manufa. Allah ya tseratar da mu daga cikin wannan bala'I wanda mun shaidi farkonsa amma ba mu san karshensa ba.

Barazanar Dokubo Asari: Bebebebebe…


A ‘yan tsakankanin nan, al’umman kasar nan sun fuskanci wasanni da hankali iri iri, sai da ta kai an daina wasa ma da hankalin, a’a kwakwalen mutane a ke bugawa tamkar kwalo daga hagu zuwa dama.
A haka nan yadda a ke kwallo da kwakwalen mutane, wasu sai kwakwalwarsu ta ci karo da dutse ta juye, sai ta yi ta diba ko yarda da kowanne irin tarkace aka zuba ma ta, ba tare da tantance tsakanin karya da gaskiya ba.
 Sauyin yanayi ya kawo mu wani zamani na rainin hankali, wanda karfin iko da mulki ba su tafiya dai dai har sai an sirka suda dabarun mallakar kwakwale da tunanin al’umma.
 Kuma zamani wanda a ke haifar da bala’I, masifa, tashin hankali, barazana, firgici domin samar da mafita ga wata matsala.
 Tun shekaru aru aru wasu kasashen duniya (musamman yammacin turai) su ke amfani da irin wannan lissafi domin cimma burinsu, misali da yadda kasar Amurka ta yi ta ruguza wasu kasashe domin bukasa tattalin arzikinta.
 Wannan bahaguwar falsafa ba ta samu wurin zama na musamman a Nijeirya ba, har sai wannan lokaci na mulkin farar hula wanda ke tafiya bisa turbar dimokradiyya. Tun mutane ba su fahimta, har ta kai ana fahimtar sabon salon, kuma kowanne shugaba idan ya zo, ya na zuwa ne da irin na shi rainin hankalin.
 Wannan dabara da wasa da hankali ne ya samar da mutane irinsu Alhaji Muhammad Dokubo Asari, wanda a ka kirkire shi a cikin dirkirarrun tsagerun yankin masu gadara da shimfidadden danyen man fetur a karkashin kasa (Neja Delta).
 Ga wadanda sunanshi kawai su ke ji, Dokubo Asari mutum ne wanda bai iya furuci ba ko miskala, hotunanshi babu abun da su siffantawa face rashin natsuwa da kamala.
 Mayaki ne (a ikirari) wanda bai san salo da dabarun fito na fito ba, shugaba ne (na ‘yan tsagera) wanda wakilcin shi ga wadanda yak e wakilta abun tir ne da Allah wadai.
 Ban dauki alkalami da niyyar hyiwa yankin Arewacin Nijeriya garkuwa ba, a’a sai don wayar da kawunan wadanda a ke son a zurma su cikin rami kuma a rufe.
 Samuwar Arewa da rashin samuwarta ya na a hannun al’umman yankin ne, idan sakaci da rashin sanin ya kamata ya sa su ka lankwashe hannuwa, su ka rungumi kaddara (kamar yadda kakanninsu su ka yi a ka yage Nijar daga Arewa), ai kuwa dole ne ta fashe a yi wasosonta.
 Barazanar ‘ya ‘yan biyuu-ahu irinsu Dokubo ba shi ne babban matsalar ba, su dai kumfar bakinsu kamar ‘yar nune ce wacce ke shaidawa al’umman yankin cewa sha-zumamu na sunsuno zaki.
 Mutum mai iyali, wanda shi ne shugaban gidanshi ba zai kuskura ya fadi wata magana wacce furta ta zai iya tarwatsa zaman lafiyan gidan ba. kai ko da kuwa rashin zaman lafiyan tsakanin gidanshi da gidajen makwabta ne.
 Ballantana kuma a ce shugaba, ba abin mamaki ba ne ga shugabannin yankin Neja Delta, tunda ba farau ba inda sakin layi ne a fadi zancen bur. Sai dai kalaman Alhaji Dokubo dole ne su girgiza mai hankali.
 Su girgiza mai hankali… da sunan wai ya tsoratar?. Haba dai, a matsayin shi dai na tsagera wanda ya yi babbar sa’ar shaidawa da kadaicin Allah, kuma ya yi imani da kasantuwar Annabi Muhammadu (S) Manzon Allah ne, cikamakin Annabawa.
 Amma da tsakar rana sai ga shi ya na cewa ‘na jimawa ina fadi, ina fada ne saboda samuwar ‘yancin mutane na kabilar Ijaw. Gaskiyar maganar kenan, kuma son ganin al’umman yankin Neja Delta da Igbo sun samu jin dadi da walwala. Saboda na hada jini da Igbo. Ni dan kabilar Ijaw ne, kuma Igbo ne, kuma dan Neja Delta. Babu ruwa na da damuwar wasu mutane can daban.’ A wata hira da jaridar Sun.
 A iyaka wannan tabargaza ta Dokubo, wanda shi a zatonshi burgewa ne da kekyashewa a tsageranci ya nuna. A bangare guda kuma bai san irin mummunan tabon da wadannan kalaman rashin dattako da natsuwa za su yi mai ba. mu dai a musulunci mun san Annabi (S) ya ce, Musulmi ‘yan uwan juna ne.
 Wannan ma ai bai ce komi ba tukunna, ga zantukanshi wadanda na nakalto kaitsaye daga jaridar Vanguard ta ranar 11 ga watan Mayun 2013. “Ina son jaddada cewa babu fa zaman lafiya da zai wanzu, ba wai a yankin Neja Delta ba, a’a a dukkanin Nijeriya, matukar Goodluck Jonathan bai ci zaben 2015. Sai dai idan kuwa Allah ya dauke rayuwarshi ne, wanda kuma ba mu fatan haka. Kamar yadda tsarin mulki ya zo da shi, Jonathan ya na da shekaru 8 cur wadanda zai yi a kujerarshi.”
 Mu a Arewacin Nijeriya, idan ka ji mutum na fadin irin wadannan soki – burutsu za ka ji ana cewa ya na zancen ‘yan tasha. Domin tasha can za ka je ka tarar da zauna gari banza, marasa tai do. Hatta ‘yan tashan cikin siyasa daidaiku ne za su iya runtse ido su yi ta soko maganganu haka.
 Sai dai kash!, mutumin fa da ya ke ta wadannan maganganu ba komin komai ba ne, kuma ba kowa ba ne shi, zaman lafiya kuma da ya k eta kurarin zai kare ai mu tuni a yankin Arewacin Nijeriya mu ka yi bankwana da zaman lafiya. Manyan jihohinmu da mu takama da su kirkirarrun tsagera ‘yan uwansu dokubo sun tarwatsa mana su da bama bamai.
 Misalin barazanar Dokubo, kamar mata ne. Kun san ai mata su na da abun mamaki a wannan duniyar, yanzun nan idan mace ta yi wani abun sai ka dauka ifiritu ne ke kimtsa mata a kwakwalwa. Su ne su ke kirkirar aljanu domin wani biyan bukatunsu.
 Wata mata ce wai aljanu sun kama ta, su kuma wadannan aljanun sikari (sugar) kawai ta ke sha sai su tashi. Yadda a ke gane aljanun sun karaso shi ne matar za ta fara wasu irin kalamai ta na fadin ‘bebebebebe’.
 Wai ashe aljanun na ta bebaye ne, don haka ko magana idan za su yi, sai dai su yi shi a tsamin baki. Ni ko har so na ke aljanun su zo, domin duk abun da su ke fadi kanzon kurege ne.
 Kawai watanni kadan sai a ka ce ai an samu maganin aljanun, amma sun ce sun daina cutar da ita, sai dai za ta rika bayar da magunguna ga mutane, ta na samun ‘yan silallan batarwa. *dariya*
 Ku saurara da kyau, wadanda kuma za su iya, su bibiya, za ku gano cewa Alhaji Dokubo Asari ya fara bebebebebe ne don a karshe ya siyar da magani, ko kuma ya riga ya ci ladar kuturu.      

Babu arzikin da ya kai Ilmi


Da yawan mutane ba su san hakikanin ma’anan ilmi ba, don haka ne ma su ke kuskurewa wurin neman shi yadda ya dace. Hatta Allah ya ce ku sanni kafin ku bauta min. duk abun da ba ka san shi ba, ba za ka iya nemanshi ba, ballantana ka same shi har ka yi aiki da shi.
 Ilmi shi ne neman sanin abun da ya shige ma mutum duhu. Wannan it ace takaitacciyar fassarar ilmi. Don haka ka neman sanin wani abu wanda ya shige ma dan Adam duhu zai iya faruwa ne kawai ga mutumin da Allah ya azurta da hankali, sannan kuma mutumin da ya iya sarrafa hankalinshi yadda ya dace.
 Ilmi shi ne tushen dukkan alheri a wannan duniya. Ilmi na da kishiya wato jahilci, a duniya dole ne mutum ya kasance dayan biyu, ko dai mai ilmi ko kuma jahili.
 Idan ka kasance daga cikin jahilai, ayyukanka wadanda su ka hada da mu’amala na yau da kullum da sauran mutane za su nuna jahilcinka a bayyane, sannan yanayin furucinka da motsinka ma jahilci zai tasirantu a cikinsu.
 Shi kuwa wanda ya kebanta da ilmi, rayuwarshi za ta haskaka ta siffofi marasa adadi, zai ga tasirin wannan ilmin kamar yadda hasken wata ke tasiri ga duhun dare. Mutanen da ya ke rayuwa a cikinsu za su kauna ce shi, sannan za su girmama shi tare da daukaka ra’ayinshi fiye da na su.
 Akwai wani mutum wai shi MATI ALJAN, mutum ne da bai san damansa da hagunsa ba (wato ba ilmin Arabi ba na Boko). Bayan wata ‘yar hatsaniya da a ka yi sai ya ke rantsuwa “Na rantse da Alkur’ani hizufi 90”, sai a ka ce mati ai Alkur’ani hizufi 60 ne, sai yace yanzu duk girman alkur’ani hizufi 60 ne?.
 Dadin ilmi kenan, wannan wani babi ne na sanin ilmin addini kacokaf, amma shi Mati da girmanshi ga aure ga ‘ya ‘ya bai sani ba saboda jahilci. Alhali a makarantun Islamiyyoyi idan ka tarad da kananan yara ‘yan shekaru 7 zuwa kasa za su fadi maka Alkur’ani hizufi 60 ne.
 Akwai karin wani misali na wani mutum (shugaba ne) ya na yiwa ‘yan kwana – kwana jawabi, ba shi da ilmi, amma kuma ya na da mulki, wannan mulkin ne ya ba shi daman ya yi jawabin kwantar da hankalin ‘yan kwana kwanan da mutane ke tsangwama. Cikin nasihan da wannan shugaba ya yi musu har ya na cewa ‘Ku yi ta hakuri, haka su Annabi Sani su ka yi ta hakuri da jama’a.’
 Na kawo wadannan misalai ne don na sake fadada al’amarin jahilci ga mai karatu. Babu wani ado ko kwaskwarima da za a iya yiwa jahilci, idan mutum jahili ne dole ne a zantukanshi ta tabbata shi din haka ne.
 Sannan kuma ba a iya siyan ilmi da dukiya, kuma ba a iya yiwa ilmi barazana da mulki ko mukami. Ilmi abu ne wanda idan mutum ya same shi, zai tasirantu a kwakwalwa, sannan ya bi jiki da furuci.
Cikin nasarorin da mai ilmi ke samu shi ne hikima. Ba kowanne zauna gari banza ba ne ke iya samun hikima. Hikimomin su na da yawa, akwai hikimar iya magana, akwai hikimar zurfin tunani, akwai hikimar iya mu’amala da mutane.
Da yawan ayyukan ta’addanci da a ke aikatawa a wannan duniyar su na kammaluwa ne da tallafin jahilai. Dalilin haka ne ma wasu malaman falsafa ‘Philosophy’ su ke cewa, duk al’umman da jahilanta su ka fi yawa, barnanta zai kazanta, sannan kuma babu fatan alheri ga wannan al’umma.
Kamar yadda karin maganar hausawa ke cewa ‘Itace tun ya na danye a ke lankwasa shi’. Al’amarin neman ilmi hakki ne mai girma da ya hau kan iyaye, wanda kuma idan ba su sauke ba, lallai a rayuwa za su kuka da ‘ya ‘yansu.
Idan da kowanne mahaifi zai dora dansa a turbar neman ilmi, lallai da kazanta da rashin tarbiyya sun karanta a cikin al’ummarmu. Amma abun mamaki sai ka ga mutum ya na fakewa da talauci a matsayin garkuwan da ya hana shi kai ‘ya ‘yanshi makaranta.
Idan ba ka iya namijin kokarin tura ‘ya ‘yanka zuwa ga neman ilmi ba, ka na fakewa da kangin talauci, lallai ya kamata ka farka daga wannan gurbataccen tunani ka fahimci cewa babu talaucin da ya kai jahilci, sannan kuma babu arzikin da ya kai ilmi.
Musamman ma yanzu yadda duniya ta ci gaba, hanyoyin neman ilmi sun sake fadada. ba dole sai an kashe makudan kudade ba wurin neman ilmi. Ci gaban kimiyya da fasaha sun zo da na’urori da hanyoyi saukaka binciken abubuwan da su ka shige ma mutum duhu.
A cikin dakinka da ‘yar kwamfuta za ka yi ta karance karance, idan ma ba ka da kwamfuta, zamani ya kawo mu da ‘yar wayar salularka za ka tsunduma yanar gizo ka yi bincike, ka yi ta karance karance a laburare iri iri na duniya.
Babu uzuri a wurin wanda bai nemi ilmi ba, saboda kofofin neman ilmin a wannan zamanin namu a bude su ke, kuma a yi shinge ga kowanne daya daga cikin wadannan kofofi ba, sai dai idan kai ne ka hana kanka. Ilmi zaki gare shi, kamar yadda jahilci ya ke da daci.

WANNAN ITA CE MATSALARMU

A wasu lokutan idan na yi dubi ga yadda al'amura su ke gudana a Nijeriya, na kan shiga cikin matsanancin damuwa marar misaltuwa.Wasu abubuwan idan su ka faru, na kan cire rai na fid da tsammanin yiwuwar dai daituwar komi kamar yadda ya dace. Tambaya ma a nan ita ce, shin menene matsalar Nijeriya?
Mafiya yawan 'yan kasar nan da za ka tunkara da waccan tambayar, da gaggawa za su amsa da cewa Nijeriya ba ta da wani matsala wanda ya wuce shugabanni.Wannan kuma ba haka ba ne, ba don matsalolin mu a dai daiku ba, da babu yadda za a yi sama da shekaru 50 mu na rayuwa cikin tagumi da matsanancin kuncin rayuwa., ba tare da tasirin namu gazawar ba.Ina yin wannan rubutun ne cikin takaici da damuwa, zukatan kaso mafi rinjaye na 'yan Nijeriya sun mutu murus. Ba a mutuwar zuciya kadai abun ya tsaya ba, gurbatar tarbiyyar da ta mamaye mafiya yawan gidaje, ga yawan mutuwar aure ko ta ina.Idan har mu na son ganin gyara, babu makawa sai mun gyara kawunanmu, mu'amala da kyautata zamantakewa.
Cikin babban kuskuren da dan adam ke aikatawa a rayuwarshi akwai rashin daukar darasi, daga tarihi ko kuma daga wadanda su ka gaba ce shi.Shi amfanin tarihi, ba wai kawai a na labarta mana ba ne, ku saurara mu yi kuka ko mu saurara mu yi nishadI. Idan da darussan tarihi sun takaita ne kan wadancan ababe da na lissafa, da babu bukatar adana tarihi, sai a rika yin tsatsuniyoyi kawai yayin da a ke son sa mutum kuka ko dariya.
Abun da zai kona ma rai shi ne yanzu al'umman da mu ke rayuwa a cikinta ba ma wai wawantar da daukar darasi daga tarihi kadai ta yi ba, a'a mun ma raina tarihin ne, sannan mu kan yi girman kai ga darussan da ke cikinsa.Idan ka tsaya ka natsu da kyau, za ka fahimci wannan. Musamman ka yi nazarin zamantakewar da ke tsakaninmu a matakin daidaiku. Ko shekara guda cur ba a yi ba da wata amarya a garin Gaya ta barbada ma mijinta maganin bera a dan wake ya ci shi da abokai su ka bakunci lahira. Yarinyar ta koka da cewa auren dole a ka yi mata, shi kuma mahaifinta ya ce sam fa shi ba auren dole ya yi ma diyarsa ba.Kwatsam! 'yan kwanakin nan sai ga wani sabon rahoto daga kano inda amarya ta aika da mijinta lahira.Ina ganin wannan sai na cewa zuciya ta, wai wadanne irin mutane ne mu ke rayuwa da su? Komi alherin da ke tattare da wanda ka ke so ka aura ma diyarka, matukar ba ta so, alherin da ke cikin janyewa ya fi na zartarwa.
Matsalarmu ta biyu a wannan lokaci ita ce rashin hakuri. Kusan kamar kowa na makale ne a wuya ya na jiran dan uwanshi. Abun da bai kai ya komo ba, sai ka ga har an kai ga zub da jini.Masana a fannin sanin halayyar jama'a sun yi fashin baki da cewa, Duk al'umman da zubar da jini ya yawaita a cikinta, su cire rai ga tsammanin wanzajjen zaman lafiya.Matsalarmu mai muhimmanci ita ce ta iyaye, yanzu tabbas iyaye sun yi kasa a gwiwa wurin daukar dawainiyar 'ya 'yansu. Ta fuskacin ciyarwa, tufatarwa, ladabtarwa, da kuma ilmantarwa.Rashin daukar wannan nauyin na yara ne ke ci gaba da samar da yawa yawan 'yan ta'adda, zauna gari banza, da sauran miyagun halaye a cikinmu. Cikin matsalolinmu akwai tsoron gaskiya, wasu lokutan ma ta na biyo mu mu na gudunta. Musamman a wannan tsakanin na siyasa, lokacin da kowanne mai nema ya buga gangar takara.Saboda lalacewar harkar siyasa a Nijeriya,  sai mutum ya tattara dukiya ta sata ko ba ta sata ba, sannan zai iya kai labari. Sai ka ga wani mutumin kirki ne, ya daya takara, amma don bai da nauyin da zai iya bin mu gida gida da sabulun naira 10 ko omon wanki, da naira ashirin ashirin, sai ka ga mun guje ma zabenshi.
A fili mu na iya fahimtar cewa mu ma azzaluman kawunanmu ne, saita al'amuran rayuwarmu ta yau da kullum, shi ne matakin magance matsalarmu muhimmiya.Mu yi tunani, wannan kwakwalwar an yalwata mu da ita ne, a ka cusa mana hankali wanda ya bambanta mu da dabbobi. Ba don mu fi so hauka Allah ya yi mana wannan Ni'imar ba, a'a sai dai don mu bambanta da su a zamantakewarmu. Mutunta juna, kiyaye darajar juna, kauna da tausayi. Tauna magana, yafiya da sauransu. Sai mun gyara kawunanmu sannan za mu iya gyara komi.

NAZARIN DABI'UN MUTANE (PERSONALITY): WANNE KA FADO A CIKI?

Mai karatu a wannan makon zan tabo fagen yanayin dabi'un mutane ne, wanda al'amari ne jai muhimmancin gaske a dukkan zamantakewa. Idan ka san yanayin dabi'ar mutanen da ka ke rayuwar yau da kullum da su, wannan zai ba ka damar kiyayewar aukuwar rashin fahimta da sabanin ba gaira ba dalili.
Shafin namu a yau zai yi bayani ne dangane da dabi'un mutane (personality). Akwai nazarori (theories) da daman gaske dangane da dabi'u (personality). Amma dai zan takaita ne ga yin bayanin guda daya watakila sauran zan yi bayaninsu nan gaba a hankali.
Akwai musayar ra'ayi da martanoni birjik dangane da dabi'a, an samu takaddamomi daga masana mashahurai tun a karnonin baya. Akwai wadanda ra'ayinsu shi ne cewa ita dabi'a a na gadonta ne daga jini, a na haihuwar mutum ne da dukkanin dabi'unsa. Yayin da wasu masanan ke ganin ai ko kadan ba haihuwar mutum a ke yi da dabi'unsa ba, koyonsu ya ke yi a hankali sakamakon tarayya da al'umma.
Wadanda ke da ra'ayin haihuwar mutum a ke yi da dabi'unsa su ne a ke kira da 'Nativist', su kuma wadanda ke da ra'ayin mutum na koyon dabi'u ne su ne a ke kira da 'Enviromentalist'.
A karkashin wadannan mabambanta ra'ayoyi guda biyu, wadanda a ke yiwa muhawararsu ta ke da 'Nature versus Nurture debate', akwai nazarori daban daban wadanda kowanne ke son tabbatar da gamsassun bayanai.
sai dai har wayau bayan dogon nazari akwai masanan da ke ganin ba zai yiwu mutum ya ce dabi'u na ginuwa ne ta bangare daya kawai, dole sai dai a kalli abun ta fuska biyu. Ta fuskacin haihuwar mutum da dabi'unsa da kuma ta fuskacin koyonsu bayan ya zo duniya.Nazarin da zan yi bayani shi ne TEMPARAMENT THEORY.Nazarin ya tafi a kan cewa gaba daya mutanen duniya dabi'unsu sun kasu gida hudu ne, ta na iya yiwuwa a samu wani da dabi'u duka hudun, amma dole sai an samu daya daga ciki wanda ya fi rinjaye. Wadannan dabi'u su ne:1.Sanguine personality. 2. Phlegmatic personality. 3. Choleric personality. 4. Melancholic personality
1. SANGUINE PERSONALITY: Masu irin wannan dabi'a sun kasance a cikin jininsu kwayoyin jan jini ya fi rinjaye (red blood). Za ka gansu su na yawan son taba mutane, su na son shakatawa, su na son harkokin more rayuwa, sun fiye surutu, su na saurin qulla abota, su na son su ga sun sa mutane annushuwa da farin ciki. A na gane wadannan masu dabi’a ne da siririyar fuska.
 2. PHLEGMATIC PERSONALITY: Su kuwa wadannan su na da kwayoyin Phlegma da yawa a jininsu. Masu wannan dabi’a sun kasance mutane masu son zaman lafiya, saukin kai sannan su na da tsauri da kiyaye dokoki. Su na da zurfin ciki, ba su damu da harkokin more rayuwa ba, su na da yawan bautan Allah. Kamanninsu shi ne, su na da fuska zagayayye (rounded), fatansu na da laushi, su na da lebe cikakke, sannan hancinsu karami ne
.3. CHOLERIC PERSONALITY: Wannan dabi'a ce ta mutanen da ke da yawaitar kwayar jini yalo (yellow) a jikinsu. Yawancinsu shugabanni ne, jagorori ne, akwai aiki tukuru. Su na yawan karatu kuma su kan ci nasara a rayuwa. Ba su da yawan abokai, su na da kiyaye lokaci saboda komi na rayuwarsu tsare tsaren gaba ne. Ba su yin kwana kwana a mu'amala. Su na saurin yin fushi saboda akwai hadafin da su ke son cimma. Su a wurinsu morewa rayuwa bata lokaci ne kawai. Kamanninsu shi ne, ba su da tsayi, su na da fadin qirji da qosasshen jiki. Da yawansu na a cikin maza, kadan a ke samu daga mata.
4. MELANCHOLIC PERSONALITY: Mutane masu yawaitar bakin kwayar jini a jikinsu. Ba su yawan yin magana, su na da gaskiya, ba ruwansu da harkokin morewa rayuwa. Sun fi son aikata komi da kansu ba su son wani yayi musu hidima. A na gane wadannan ta hanyoyi kamar haka: idanuwansu na da duhu, sannan za ka ga kansu na wani lilu.
 Ta na iya yiwuwa a samu wani mutum wanda za a ga jifa jifa daga cikin wasu dabi'unsa a dukkan hudun, amma maganar gaskiya ita ce, dole ne ya zama akwai inda dabi'un nasa su ka fi karkata.
Da fatan mai karatu ya gano wacce dabi'a ta fi rinjaye a rayuwarshi.

Ya a ke nuna wa MUTUM kauna?


Mai karatu a wannan makon zan karkata sannan in dai dai ta don yin bayani dangane da kauna. Da yawan mutane, musamman hausawan da ba su san hausa ba (sai dai sun iya furuci da fahimtar harshen).
 Da yawa a na kuskure kalmomin So da kauna. Alhali wasu abubuwa ne mabambanta guda biyu, wadanda kuma kowannensu ke taka rawarshi tare da tasiri na daban a cikin zukatan mutane.
 So wani halitta ne mai karfi wanda ke ruruwa a cikin zuciya. A falsafance a na kallon So a matsayin wani al’amari wanda ke tattare da jin kai, kusanci, da kuma aminta da juna.
 Kusan gabakidaya addinai masu da’awar bauta sun tafi a kan hanyar tarbiyyantar da mabiya soyayyan juna. A na iya kallon So a matsayin wani abu wanda za ka nuna na damuwa ga wani (ko ga kanka) bisa zabin kanka.
 A kamus din fassarar kalamai na masana ilmin halayyar jama’a, sun yiwa Soyayya fassara da wani al’amari wanda ke kunshe da mabambantan abubuwa, daga ciki akwai yanayi, dabi’a, gamsuwa, don janyo hankalin wani.
 Saboda bambance bambancen da ke tsakanin al’ummu na yadda su ke kallon al’amura, shi ne dalilin da ya sa a al’adance kowa ya na tafiyar da rayuwarshi ne dai dai gwargwadon yadda al’adar garinsu ya shardanta.
 Za ka iya samun wasu gungun mutane wadanda su al’adarsu ce ta zo da halascin Mace ta auri mazaje da fiye da daya, kuma idan ma ba ta aikata hakan ba, kamar ta yi sabo ne.
 Auren Mazaje da yawa al’ada ce mai karfin gaske ga duk wata mace da ta tsinci kanta a kabilar Nayar da ke garin Kerala a Kudancin Indiya. Dole ne ta yi aure mazaje da daman gaske wadanda a al’adance su ke kira da Sandbanham.
 Wannan ya saba da wasu al’adu mafiya rinjaye a duniya, wanda dolen dole Mace a zamantakewar aurenta ta kebanta ga mutum guda, ba mazaje ba kamar waccan al’adar da na misalta.
 Ban da wannan, akwai misalai da yawan gaske wadanda ke nuni da bambancin yanayin tafiyar da rayuwa a al’adun al’umma. Idan dan wata al’ummar ya ga dabi’ar wasu al’ummun sai ya yi ta mamaki, ya na fadI a zuciyarshi ‘Anya mutane ne kuwa?’.
 Dalilin da ya san a kawo wannan misali na al’adu shi ne don na sake fito da maudu’I na fili. A dukkanin mafi yawancin al’adun duniya sun samu kansu ne dalilin kaunan juna. Duk mutanen da su ka wayi gari babu kaunar juna a tsakaninsu, ba da jimawa ba za su zama tarihi.
 Tunda a can baya na yi bayani mai tsawo dangane da Soyayya, kuma a dan iya abun da na iya bayyana da shi, na san a na iya fahimtar me Kalmar So ke nufi. Don haka ne zan yi kokarin fayyace bambance bambancen da ke tsakanin wadannan kalmomi masu kamanni da juna.
 Soyayya na kulluwa (a bisa mafi saukin fahimta) tsakanin jinsin maza da mata, wanda kuma a wasu lokutan idan tafiya ta yi tafiya, sai a kai ga aure.
 Ita kuwa kauna ta fi karfin nan, ta girmi a kira ta ko a kwatanta da wani abu wanda ke kulluwa tsakanin Maza da Mata. {auna ita ce rayuwa, kuma duk zuciyar da babu wadataccen kauna a cikinta, wannan matacciyar zuciya ce wacce kullum ta ke a cikin damuwa da nadama.
 A na fara samun tarbiyyar kauna ne tun a lokacin da a ka haifi jinjiri, sannan ne mahaifiya za ta fara tarbiyyantar da danta kauna, za ta kaunace shi ta yadda kukanshi cikin tsakar dare na iya zama sanadiyyan gushewar baccinta har wayewar gari.
 Saboda tsananin kaunar mahaifiya ga jinjirinta, zai yi fitsari da bayan gida a lokacin sanyi, amma kuma damuwarta ba wai ya bata ta ba ne, babban damuwarta kawai sanyi zai iya cutar da yaron. Sannan kuma komi tsananin sanyi haka nan za ta tsaftace fitsarin jinjirin da ruwa mai sanyi.
 Idan da a ce mutum zai rika zaunawa, ya natsu ya rika tunanin irin kaunar da mahaifiya ke nunawa danta (tun a lokacin da ya ke jinjiri) da babu wanda zai zama mai ciwon hassada, bakin ciki, munafunci, mugunta da duk wasu munanan halaye.
 Sannan kuma da mutane za su rika kulla zamantakewar aure bisa turbar kauna ba Soyayya zalla ba, da an yi bankwana da yawan mace – macen aure.
 A yau mutane su na wani irin zaman munafunci ne wanda kuma al’amari ne mai bakanta rai. Za ka ga mutum ya na yi maka faran faran, kuma ya rika rayawa tare da furucin shi mai kaunarka ne alhali kuma mu’amalarku ta na karya ta kasantuwar haka.
 Idan har ka na tare da mutum, ka na aikata wasu munanan dabi’u amma kuma ya kasa jurewa ya kwakkwafa ka don ka dawo ma turbar gaskiya, to wannan mutumi ko kadan ba ya kaunarka.
 Duk inda ba za a iya fede ma ka gaskiya ba duk dacinta a yayin da ka yi ba dai dai ba, wannan ba wurin zama ba ne, ko kuma shi ba abokin tafiya ba ne.
 Idan ka na kaunar mutum, a shirye ka ke kowanne lokaci ka fadi mishi gaskiya, idan ta kama ka ladabtar da shi don ya dawo hayyacinshi ko da kuwa hakan na iya zama sanadiyyan da zai fara jin haushinka, kai dai kawai ka yi don Allah.

ZABEN 2015: YIWUWAR DAWOWAR SOJA


KUri'u su na da tasirin gaske a dukkanin siyasar da asasinta ya ginu a kan turbar dimokradiyya. Sai dai, wani abu da ya kamata mu sani shi ne kuri'u ba su ne ke ayyana sakamako ba 100 bisa 100.
Kowacce kasa ta na da na ta hanyoyin cimma sakamako a matakin karshe. Misali, a kasar Amurka, komi yawan kuri'un da dan siyasa zai samu ba za su cika mishi burinshi na lashe zabe ba. Dole ne sai wannan shugaba ya na da goyon baya daga Yahudawa. Wadanda su ne ke juya akalar siyasar Amurka. Ko da kaso 70 na mutanen Amurka sun mika kuri'unsu ga dan takara, matukar bai da alaka ko kusanci da wadannan kebabbun Yahudu, sun yi a iska.
Haka nan a kasar jamhuriyar Musulunci ta Iran, tun kafin ma zaben, akwai majilisar koli ta malamai wacce ke tantance 'yan takara. Su a na su bangaren ma, idan wani mai tarihin matsala ya fito takara, su ka gano wani tabo da ya ke da shi wanda ya saba da tushen ka'idojin kasar. Tun a takun farko za a zabge shi kafin ma a yi ruwan kuri'u. Don haka duk wanda ya fado cikin 'yan takara to majalisar malamai sun aminta da shi.
Na kawo wannan ne da wadancan kasashe biyu mabambanta, don in yi sharar fage ga irin dabi'ar siyasa, zabe da kuma kuri'un al'umma.
Shin kuri'u na iya kawo mutum ga mukami a siyasance, musamman mukamin da ya fi kowanne a kasa ta shugaban kasa.
Zan takaita rubutun ne a iyaka Nijeriya, saboda la'akari da gabatowar zaben gamagari a 'yan kwanaki masu zuwa.
Maganar gaskiya ita ce, mutum bai bukatar a yi mishi dogon bayani kafin ya gane cewa akwai wasu hannaye da ke jujjuya al'amuran Nijeriya, ban da ikon shugaban kasa. Wannan wani abu ne da ke bayyane a fili.
Wadannan mutanen boye ne ke murda murdar ganin wanda su ke so ya samu mulki, kuma in ka zamo shugaba dole ka taka rawa yayin da su ka kada ganga. Kamar misali, tarihi ya nuna cewa kusan duk wani juyin mulki da a ka yi ko za a yi, sai ya kasance akwai hannun wasu masu fada a ji daga wajen kasar, kuma a waje a ke shirya shi.
Hatta daga cikin 'ya 'yan jam'iyyar PDP masu mulki, ba su san cewa ba tsagoron karfin jam'iyyarsu ba ne ke ba su damar ci gaba da mulkar Nijeriya. Shi ne ma ya sa su ke cika bakin sai sun mulki kasar na sama da shekaru 60 ba tazara.
Zaben da ke fuskantarmu a wannan sabuwar shekara, alamu na nuna zai yi wahalan gaske kuri'u su yi aiki. Za a buga zabe ne tsakanin wasu ra'ayoyi wadanda ke karo da juna.
A matakai na kasa-kasa, nan ne kuri'u ke iya taka rawa. Misali, a zabukan Kansiloli, ciyamomi, 'yan majalisun jiha, wasu wuraren ma har 'yan majalisun tarayya, wakilai, da gwamnoni.
Kamar yanzu da a ka samu gamayyar jam'iyyu su ka samar da jam'iyyar APC, za ka samu a kananan kujeru 'yan siyasar da a ka tsayar takara a jam'iyyar sun cinye, saboda guguwar Buhariyya da APC.
A wadannan matakan ma kuri'u su na aiki ne a lokacin da son ran masu ikon juya zabe bai yi karfi a kujerun ba. Ba wai tayar da jijiyar wuya ba, ko kafawa a tsare, ko da mutanen yankin za su mutu mafiya yawansu, sai an murgude.
Misali a nan, a zaben 2011 a jihar Kaduna, da bakin bindiga a ka ayyana marigayi Yakowa a matsayin Gwamna. A na gab da sanarwa, sai kawai sojoji su ka fara harbi a sama a lokaci guda kuma gidajen rediyo na sanar da dokar hana zirga zirga, sannan a ka sanar da sakamakon zabe. Kun ga kenan, wannan karfa karfa ta nuna cewa ba kuri'u ba ne su ka yi aiki, karfin ra'ayi da iko ne ya yi aiki.
Wannan zaben mai zuwa, hatta masu juya al'amuran kasar sun san wani babban al'amari na shirin faruwa. Na farko idan su ka aminta da guguwa da sabon yayi na APC, har su ka aminta da mika mulki ga Buhari (idan ya lashe zabe), kasar na iya fadawa yakin bangaranci, saboda tun yanzu wasu rikitattun mutane a yankin Kudanci sun fara sumbatun za a yi fito na fito idan Jonathan ya ruguzo.
Haka kuma idan Jonathan ya ci, mutanen Arewa babban abun da zai zo a ransu, shi ne an murgude za be ne, kuma ba za su yarda ba. Har ma da wasu daga mutanen yankin Yarbawa. Wannan zai haifar da bore da zanga zangar kin jinin gwamnati.
Idan har kasar ba ta fada ma yakin bangaranci ba, tsakanin Kudu da Arewa, za a yi bore. Wannan rashin gamsuwa daga mutane, da rashin gane bakin zaren daga masu juya kasar, idan sun ga dama sai su ingizo wani soja, wanda su ka kimtsa don gudun ko - ta - kwana, ya sanar da juyin mulki.
Mu na fatan ba za a yi yakin basasa ba. Haka nan mu na fatan ba za a yi magudI ba ballantana a yi bore. Mu na rokon Allah ya kiyaye rayukan jama'a. Wannan kawai hasashe ne! Mu hadu mako mai zuwa.

AURE BA WASA BA NE


Allah sarkin iko, shi ne mai zamani kuma mai bayar da aron numfashi ga duk wanda ya ga dama. Haka duniyar ta gada, wasu a tsawaita musu kwana, wasu kuma a gajarta musu. Wadanda a ka tsawaita ma kwana a duniyar nan su na gamuwa da gane gane iri iri, wasu na da zuciyar iya jurewa masifu da fargaba, a bangare guda kuma takaici na iya hallaka wasu.
 Wadanda ke raye a wannan zamani na gane gane. Wasu al’amjuran ma sa mutu m ya yi zaton almara, tatsuniya ko hikaya ne.
 Zamani ya zo da abubuwa da daman gaske, wasu masu kyau wasu kuma marasa kyau, don haka ne ma mafi kyawun shawarar masana shi ne kowa ya yi riko gam da al’adarshi ba tare da aro wata al’ada daga wani wuri ba.
 Al’adun mutane na da ban mamaki, a wurin wasu kazantarku ita ce halas dinsu, ku kuma tsaftataccenku shi ne gurbataccensu.
 Kafin na ci gaba da koro bayani sai na bayar da misalin irin bambance bambancen da ke tsakanin al’adu domin mu sa ke fahimtar yadda al’amarin ya ke da haske.
 A ‘yan kwanakin nan gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da batun auren jinsi daya, hani ga dokar da za ta bayar da dama ga namiji ya auri namiji, haka nan ma mace ta auri mace ‘yar uwarta.
 A wasu kasashen turai, sam wannan dabi’ar dabbobin ba abun kyama ba ne har ma sun lamince ma masu sha’awa, sun shigar da ita cikin kundin tsarin mulkinsu a kan halascin yin irin wannan aure. Wannan ya nuna wa sauran al’ummar duniya da ke tsananin kyamatar wannan halin dabbanci cewa al’adar wadancan turawa ta yi hannun riga da irin dattijuwar al’adarsu.
 Haka nan idan mun dawo da misalinmu gida Nijeriya, mu na iya fahimtar bambancin al’ada a tsakanin kabilun da ke kudancin kasar da kuma kabilun da ke Arewaci.
 Kaitsaye a na iya kawo wasu kabilu masu al’adar sai mace ta yi ciki a waje kafin nan a daura mata aure. Irin wadannan kabilu su a wurinsu namiji ba zai yi aure cikin duhu ba, dole ne sai ya yi gwajin shin matar da ya ke son aure ta na haihuwa ko kuwa juya (marar haihuwa) ce?.
 Wanda irin wannan al’ada idan mu ka dauko shi mu ka zuba a cikin jerin al’adun mutanen Arewacin Nijeriya sai abun ya yi wani irin banbarakwai ba ko kyawun gani ballantana ji. A Arewa idan namiji na son yarinya da aure, dole ne sai ya nemi izinin iyayenta, sannan kuma bai halasta gare su su kebe ba a killataccen wurin da ba mutane ba yayin zance ko da kuwa ya biya kudin sadaki, matukar ba a shafa fatihar daurin aure ba.
 Da wadannan ‘yan misali na ke son jaddadawa mai karatu cewa duk wata al’adar da mutanenmu (‘yan arewa) ke sha’awar aro wa daga wasu al’adun abun haushi ne da kyama. Saboda idan da wani zai dauki ta mu al’adar ya kai inda mu ke aro tasu ba za su aminta da ita ba, fito na fito ma za a yi da ita duk tsaftarta.
 Abun na da matukar ban mamakin gaske yadda al’amarin aure ya kicime a wannan yanki (arewa) mai dadadden tarihin tsaftatacciyar al’ada, dattako, dabi’un kirki da kuma sanin ya kamata.
 Lalacewar tarbiyyar ma akwai wacce idabn da a nan abun ya tsaya a na iya cewa da saukI ko kuma a ci gaba da fatan samun canji cikin gaggawa, amma fa.
 Idan mace ba ta yi aure ba, a al’adarmu a na yi ma kaifin tunaninta uzuri yayin da ta aikata wasu laifukan, amma ita kuwa matar aure, uzurin kenan a janyo hankalinta da cewa, ‘in an girma a san an girma. Shekaru kadan za ki tara ‘ya ‘ya da jikoki.”
 Don haka ya na da kyau matan aure su natsu da kyau su fahimta, duk wani abu na rashin mutunci ba nasu ba ne. saboda duk lokacin da ki ka jefa kanki cikin sahun marasa mutunci, wannan bakin fentin sai ya mamaye ilahirin ‘ya ‘ya da jikokinki.
 Akwai matan da natsattsu ne amma mu’amalarsu da kawaye, sai su fara badalolin babu gaira ba dalili. Haka kuma akwai matan da zuciyarsu tas ta ke babu birbishin yaudara da cin amana a cikinta, amma da zaran sun fara ta’ammuli da yanar gizo sai shaidan ya yi musu saka.
 Guguwar wayoyin salula masu dauke da yanar gizo da kuma sauran kafofin sadarwa ‘social network’ ya jefa ma’aurata cikin wani mawuyacin hali. Da yawa aurensu ya tsinke, wasu kuma an samu giftawar zargi, wasu kuma an rasa zaman lafiya rikicin yau daban na gobe ma daban.
 Sai ka ga mata da mijinta, ba kunya ba tsoron Allah ta na yin hira da wani jibgegen katon da ba muharraminta ba. Wasu matan sai su ce ai gaisuwa ne kawai kuma daga ita ba wani abu. In ji wa?
 Ke ki na ganin tarbiyyar kwarai ce da aurenki ki rika gaisawa da wasu mazan da ba ‘yan uwanki ba a waje?. Idan kuma an gaisa din, sai hira mai ma’ana ta shiga tsakani ki ka biye a ka ci gaba, wannan kuma me ki ka aikata?
 Ba ma wannan ba, da yawan matan aure su na amfani da kafafen sadarwa na yanar gizo su na ha’intar mazajensu. Da yawa su na tattara samari, musamman matasa wadanda su ke soyayya da su (soyayya a kan aure).
 Wannan wane irin zamani ne haka?. Ke da akwai igiyar aure sargafe a wuyanki, me za ki yi da shafukan sadarwa irinsu Facebook, twitter, badoo, bbm, 2g0, mxit, twitter da sauransu?. Ba wai yanar gizon ba ne ba a so ku yi aiki da shi don ku na matan aure, amma ya na da kyau ne ku mutunta aurenku.
 Masana a fannin sanin halayyar jama’a dai sun ce ita zuciya wata bahaguwar aba ce wacce ke gamsuwa da sake sake masu kyau da marasa kyau. Idan ma tsarkin niyya ki ke ‘chatting’, ki na iya haduwa da shaidanin da zai iya dagula miki lissafi, to me zai hana tun farko ki watsar ki huta, aure fa ba wasa ba ne. Allah ya sa a gyara.