A wata taqaddama mai sarqaqiya, an ce kowanne mutum ma mugu ne, an ce kowa na da nau’in mugunta a cikin jininshi, sai dai wani mugun ya gawurta fiye da wani.
Ma’anar mugunta a fannin ilmin zamantakewa da sanin halayyar jama’a shi ne cutar da mutane bisa ganganci. Dalilin da ya sa mu ka mayar da hankali wurin karantar mugunta shi ne bisa la’akari da yadda mugaye su ka yi wa duniya yawa.
Saboda qoqarin ganin an fahimci mugunta da nau’o’inta, masana a wannan fanni sun kasu kashi uku; ‘yan sahun farko su ne wadanda su ka tafi a kan cewa mugunta halitta ce wacce a ke haifo mutum da ita ko kuma a ke iya gadonta. ‘yan sahu na biyu kuma su ne wadanda ke da ra’ayin cewa babu ruwan dabi’a ko gado da muguntar mutum. A yanzu an samu kaso na uku, wadanda su kuma ke ganin mugunta ta tattara abubuwa da yawa, ba abu guda daya ba ne ke zama dalilinta.
Akwai mugunta wacce ta qumshi cutar da gangar jikin mutum – misali mangari, naushi, caccaka wuqa, ko kuma harbi da bindiga ko kibiya. daya sashen mugunta shi ne wanda bai qumshi cutarwa kaitsaye ga gangan jikin mutum ba. Irin wannan muguntar sun hada da ta fatar baki, irinsu yiwa mutum ihu, rantsuwa bisa shaidar zir. Cikin irin wannan muguntar har da yin gulma domin cin zarafin wani mutum. akwai kuma wata samfurin mugunta wacce ba ta buqatar magana da fatar baki, kawai sai dai a yi amfani da alami, misali fashewa da dariya yayin da wani ya shigo wuri. Toshe hanci a yayin da wani ya gifta, da dai sauransu.
Zan bibiyi wadannan mabambantan ra’ayi ta yadda hatta mai karatu zai iya fahimtar daga ina mugayen da ke zagaye da shi su ka samo muguntarsu. Idan kuma kai ne mugun, bayan karanta musabbabin mugunta za ka so ka yi qoqarin daqile ta ko rage tasirinta a kanka.
Wadanda su ka ce mugunta a na haihuwar mutane ne da ita sun tafi a kan cewa akwai wata qwayar halitta mai suna ‘Thenatos’ wacce a ke haihuwar kowanne dan Adam da ita. Ita wancan qwayar halitta ne ke ingiza mutane wurin aiwatar da duk wani nau’in mugunta a kan mutane.
A wurin masu irin wancan fahimtar sun ce ita qwayar halittar ‘Thenatos’ an halicci mutum ne da ita a matsayin wani sindari da zai rusa shi. A maimakon mutum ya bari wannan qwayar halitta ta ‘Thenatos’ ta rusa shi, sai a riqa yin amfani da ita wurin cutar da mutane, dabbobi ko wasu halittun da ke kusa da shi.
Masanan sun ci gaba da cewa, idan a cikin mutane ka ga wani mutum wanda bai fiye aikata mugunta ba; ire iren wadannan mutanen su na danne waccan qwayar halittan ne ta yadda sai dai ta ci gaba da cutar da su.
Babban misali a nan shi ne, mutumin da ya qware a mugunta ba ya buqatar sai an tsokane shi ko an aikata wani aiki sannan zai aikata muguntan. Zai iya daukan mota ya hau titi ya na mugun gudun da zai riqa tsoratar da mutane, wasu lokutan ma har ya hau ta kan wasu. Ka ga kenan wannan mugun bai buqatar wani dalili kafin ya aikata. Amma akwai a cikin mutane wadanda ko ka nemi rikicinsu, za su danne su bar komi ya wuce. Za ka ga wani, an zo da mota an yi mishi tuqin ganganci har ma a yi mishi barna, amma wannan ba zai sa shi ma ya mayar da ganganci ba balle ya aikata barna.
bangaren wadanda ke ganin babu wata alaqa tsakanin mugunta da qwayar halitta sun bayyana ne sakamakon martani da raddi da su ka dabaibaye wancan ra’ayin na farko. Su kuma wadannan sun tafi ne a kan cewa mutum na zama mugu ne sakamakon tursasawa. Ma’anan tursasawa a nan shi ne a kange mutum daga cimma wani muradi na shi ko kuma a tauye mishi wani haqqi da ya ke ganin na shi ne.
Masu wannan ra’ayin na alaqanta mugunta da tursasawa sun tafi a kan cewa yanayin yadda za ka tursasa mutum yanayin irin samfurin muguntan da zai aikata maka. Shi ya sa a wurinsu mugunta ta fi yawa a wurin wadanda ba su da aikin yi, da wurin wadanda ba su da kudi, da kuma wurin wadanda su ka sha kaye a fagen soyayya.
Misali a nan shi ne, idan har a ka samu yawan matasa wadanda ba su da aikin yi a gari, wannan rashin aikin yi shi ne zai tursasa matasan su riqa sa kansu a cikin rikice rikicen da za su iya kaiwa ga salwantar rayuka, qone qone da sace sace.
Haka kuma idan mutum biyu su na neman budurwa daya. Sai na farko ya samu dacen sace zuciyar yarinyar, har ta kai idan na biyun ya zo zance, sai na farkon (wanda ya sace zuciyarta) ya zo ya janye ta gefe, sannan kuma su yi ta sheqewa da dariya; wannan irin cin fuska da su ke yi mai zai tursasa shi ya aiwatar da kowanne irin nau’in mugunta a kansu.
Shi ma wannan nazarin na alaqanta mugunta da tursasawa ya sha raddi da martani; martanin ne ma ya samar da wani nazarin dangane da mugunta, wanda ya tafi a kan cewa babu wani abu qwaya daya tak da ke zama musabbabin mugunta. A wannan fahimtar, mugunta babu ruwanta da qwayar halitta, sannan babu ruwanta da tursasawa. Ita mugunta a na koyonta ne kamar yadda a ke koyon sauran dabi’u. ta hanyoyin da a ke bi a koyi sauran dabi’u ta su kuma a ke bi a koyi mugunta.
Idan mutum ya fiye kallon fima fiman mugunta, babu makawa zai fara gina dabi’ar mugunta. Wanda a kodayaushe bai da aiki sai kallon fima fiman da Amurkawa ke yi, a na kwano da mota a na rusa gidaje da qaddamar da mugunta iri iri, akwai yiwuwar duk ranar da wannan mutumi ya dauki mota ya yi qoqarin gwada abin da ya ke kallo.
Kamar yadda mu ke koyon mu gaisa da mutane, haka nan mu ke koyon mu mari mutane. Kamar yadda mu ke koyon mu yi wa mutum murmushi haka nan mu ke koyon mu zare wa mutum ido don ya ji tsoro. Saboda haka idan a ka ce wai tursasawa ne ke janyo mugunta, sai mu ce ai akwai mutanen da mu ka sani wadanda za a tursasa su a kai su bango amma su hadiye fushinsu. Haka kuma yadda a ke samun mugaye a cikin talakawa haka nan a ke samu a tsakanin masu dukiya. Mugunta ba komi bace face wata dabi’a wacce mu ke koyo a muhallin da mu ke rayuwa; idan mu ka tsinci kawunanmu a tsakiyar mugaye, za mu ginu da dabi’ar yi wa mugunta kallon abu me kyau. Mu hadu mako mai zuwa!
Wannan shafi an samar da shi ne domin watsa rubuce rubuce na ilmantarwa da fadakarwa musamman wadanda su ka shafi IIlmin sanin halayyar dan Adam da zamantakewa (Sociology). Alqalamin shafin zai fi karkata ga rayuwa, musamman na matasa. Sunan shafin ya samo asali ne daga jaridar Leadership Hausa. Shafi ne wanda ke kawo rubuce rubucen marubuci Sulaiman Bala Idris (ISB DAURAWA) +2347036666850
Monday, 7 September 2015
Mu Fahimci Dabi’ar MUTUM 'ATTITUDE'
Matsalolin da ke tattare da yawancin ma’aikatu, masana’antu, cibiyoyi da hukumomi ba komi ba ne face matsalar rashin sanin dabi’un dan Adam. dabi’a aba ce me wahalan sha’ani, kadan ne daga cikin mutane su ke yin mu’amala da mutum a lokaci guda kuma su ke karantar dabi’arsa. Sau da yawa kawai mu’amala da fankon mutum mu ke yi, ba tare da nazarin dabi’arsa dangane da abubuwa ba.
dabi’ar mutum ne ke taimakonsa ya fassara yanayi, kuma duk ta yadda ya yi fassaran yanayi a haka zai tafiyar da shi, kuma da wannan fassarar ne zai duba ya gani shin wacce irin mu’amala zai yi a dai dai lokacin.
dabi’un mutane sun bambanta, sai dai a wasu lokutan a kan samu wani babban al’amari wanda ke zama sanadin haifarwa da mutane dabi’a iri guda. Misali a nan shi ne, a shekarar 2003 lokacin da qasar Amurka ta shirya za ta yaqi qasar Iraqi, mutanen qasar Amurka sun yi ta zanga zangan Allah wadai da wannan yaqi da a ke son gabatarwa. Wannan ya nuna mana cewa, mutanen Amurka sun gaji da yaqe yaqen da qasar ke shiga, saboda haka yawan yaqin da qasarsu ke yi sai ya haifar musu da dabi’ar qin jinin yaqi.
Akwai wasu abubuwa da dabi’ar mutum ne kadai ke kai shi ga aikata su. Na farko, dabia ce kadai ke sa mu qaunaci mutum ko mu qi shi, ita ke sa mu ji mu na son wasu gungun mutane ko qungiya. Haka nan dabi’arka ce kadai za ta iya zartarwa ka danganta kanka da qungiya; kamar misali idan dabi’arka ba ta qaunar tsiraici da kallon batsa, babu yadda za a yi ka kasance ma’abocin kallon fima fiman da ‘yan Kudancin Nijeriya ke yi a yanzu ‘Nigerian Films’, saboda dabi’arka ba ta son kallon irinsu, ko da bisa kuskure ka zo inda a ke kallo, yanayin fuskarka da yadda ka ke yi, zai nuna cewa ka ginu da dabi’ar qin irin wannan fima fimai.
Na biyu shi ne, da dabi’a mutum ke dubawa ya ga shin idan ya aikata wani aiki me zai biyo baya? A nan za mu iya cewa saboda son biyan buqatar mutum ya na iya aikata dabi’un da zasu kai shi ga cimma muradunsa . Misali, mutumin da ya hango diyar wani ya na so, zai yi qoqarin ko ta wanne hali ya riqa aikata dabi’u masu kyau a wuraren da ya ke tsammanin mahaifin yarinyar ko wasu makusantanshi. Ba kawai biyan buqatun mutum ba, da dabi’a mutum ke kiyaye abubuwan da za su iya kasancewa barazana gare shi. Misali a nan shi ne, bayan da a ka samu sabuwar gwamnati a Nijeriya; da yawan manyan mutane sun fara sassauta dabi’unsu na almubazaranci, da almundahana saboda gudun kar Shugaban qasa Buhari ya yi sukuwa a kansu. Wannan dabi’ar ta ginu ne saboda tsoro.
Na uku, a sau da yawa za ka ga wasu mutane na aikata abu babu kyawun gani. Su a wurinsu dabi’arsu ce ke nuna musu cewa wannan abu da su ke aikatawa dai dai ne. Abu daya ne ke dai daita dabi’ar mutum zuwa mai kyau kuma ta-gari, shi ne ilmi. Ilmi na da muhimmancin gaske wurin tasiri ga dabi’ar mutum. Misali a nan shi ne, za ka ga mutumin da bai je makarantar jami’a ba ko gaba da sakandare, zai tashi da wata irin dabi’a ta gani – gani ga duk wata qabila da ba ta shi ba. Amma a lokacin da mutum ya samu damar halartar makarantun gaba da jami’a, inda kusan kowacce qabila ta na da ‘ya ‘yanta a matsayin dalibai, bayan dogon lokacin da mutum zai dauka ya na karatu tare da mu’amala da mutane daga qabilu daban daban, za ka ga ya samu chanji a dabi’arsa daga qin jini ko gani – gani ga wasu qabilun da ba nashi ba.
Na hudu, dabi’ar mutum ne ke ba shi dama ya bayyanawa duniya ko shi wanene, dabi’arsa ce ke ba shi daman bayyana al’adarshi da irin halayenshi. Kamar misali, a shekarun baya da su ka shude a jihar Kano, idan ka ga mutum da jar hula, babu tantama wannan jar hula na alamta qauna ne ko shauqin Malam Aminu Kano. A yanzu kuma idan ka ga mutum da hula a Kano, mutane na saurin fassara shi ne da kasancewa dan Kwankwasiyya. Wannan ne ya sa da yawan dattawa (tsofaffi) a cikin garin Kano su ka watsar da jajayen hulunansu (Na Malam Aminu Kano) saboda su ba’yan kwankwasiyya ba ne, kuma ba su so a fassara su a haka.
Duk da dabi’a ba wata aba ba ce da a ke iya gani da ido, ko a taba, amma a na iya auna ta. Wannan ba sabon abu ba ne. idan ka na so ka fahimci inda dabi’ar mutum ta dosa dangane da wani al’amari bari ka ji yadda a ke auna dabi’a. Akwai wasu hanyoyin auna dabi’a da yawan gaske wadanda mu ke amfani da su, amma mafi sauqin ciki zan yi bayani a kai.
Kamar misali, ka na so ka fahimci shin menene ra’ayin mutum dangane da auren zawarawa da wasu gwamnoni ke bayarwa. Sai ka yi mishi tambaya kamar haka; Shin ka na goyon bayan auren zawaran da gwamnati ke jagoranta? Kai za ka qayyade amsoshin da mai amsawa zai zaba, ba wai za ka barshi ya yi ta zubo bayani ba ne. misali sai ka bashi zabi biyu; Eh ko A’a.
Duk amsar da wanda a ka tambaya ya zaba a cikin biyun, da su za ka auna dabi’arsa dangane da auren zawarawa. Idan ya zabi EH. Shi kenan ka gano cewa dabi’arsa dangane da auren zawarawa ta goyon baya ce, wannan zai sa ba za ka riqa fargabar yin maganan auren zawarawa da shi ba, musamman muhimmancinshi da kuma amfaninshi. Idan kuma ya zabi A’A, ya na nuna dabi’arsa ba ta qaunar auren zawarawan da a ke yi, shi zai sa ka kiyaye yawan matsawa a kan auren zawarawa a duk wata tattaunawarka ko mu’amalarka da wannan mutumin. Mu hadu mako mai zuwa
dabi’ar mutum ne ke taimakonsa ya fassara yanayi, kuma duk ta yadda ya yi fassaran yanayi a haka zai tafiyar da shi, kuma da wannan fassarar ne zai duba ya gani shin wacce irin mu’amala zai yi a dai dai lokacin.
dabi’un mutane sun bambanta, sai dai a wasu lokutan a kan samu wani babban al’amari wanda ke zama sanadin haifarwa da mutane dabi’a iri guda. Misali a nan shi ne, a shekarar 2003 lokacin da qasar Amurka ta shirya za ta yaqi qasar Iraqi, mutanen qasar Amurka sun yi ta zanga zangan Allah wadai da wannan yaqi da a ke son gabatarwa. Wannan ya nuna mana cewa, mutanen Amurka sun gaji da yaqe yaqen da qasar ke shiga, saboda haka yawan yaqin da qasarsu ke yi sai ya haifar musu da dabi’ar qin jinin yaqi.
Akwai wasu abubuwa da dabi’ar mutum ne kadai ke kai shi ga aikata su. Na farko, dabia ce kadai ke sa mu qaunaci mutum ko mu qi shi, ita ke sa mu ji mu na son wasu gungun mutane ko qungiya. Haka nan dabi’arka ce kadai za ta iya zartarwa ka danganta kanka da qungiya; kamar misali idan dabi’arka ba ta qaunar tsiraici da kallon batsa, babu yadda za a yi ka kasance ma’abocin kallon fima fiman da ‘yan Kudancin Nijeriya ke yi a yanzu ‘Nigerian Films’, saboda dabi’arka ba ta son kallon irinsu, ko da bisa kuskure ka zo inda a ke kallo, yanayin fuskarka da yadda ka ke yi, zai nuna cewa ka ginu da dabi’ar qin irin wannan fima fimai.
Na biyu shi ne, da dabi’a mutum ke dubawa ya ga shin idan ya aikata wani aiki me zai biyo baya? A nan za mu iya cewa saboda son biyan buqatar mutum ya na iya aikata dabi’un da zasu kai shi ga cimma muradunsa . Misali, mutumin da ya hango diyar wani ya na so, zai yi qoqarin ko ta wanne hali ya riqa aikata dabi’u masu kyau a wuraren da ya ke tsammanin mahaifin yarinyar ko wasu makusantanshi. Ba kawai biyan buqatun mutum ba, da dabi’a mutum ke kiyaye abubuwan da za su iya kasancewa barazana gare shi. Misali a nan shi ne, bayan da a ka samu sabuwar gwamnati a Nijeriya; da yawan manyan mutane sun fara sassauta dabi’unsu na almubazaranci, da almundahana saboda gudun kar Shugaban qasa Buhari ya yi sukuwa a kansu. Wannan dabi’ar ta ginu ne saboda tsoro.
Na uku, a sau da yawa za ka ga wasu mutane na aikata abu babu kyawun gani. Su a wurinsu dabi’arsu ce ke nuna musu cewa wannan abu da su ke aikatawa dai dai ne. Abu daya ne ke dai daita dabi’ar mutum zuwa mai kyau kuma ta-gari, shi ne ilmi. Ilmi na da muhimmancin gaske wurin tasiri ga dabi’ar mutum. Misali a nan shi ne, za ka ga mutumin da bai je makarantar jami’a ba ko gaba da sakandare, zai tashi da wata irin dabi’a ta gani – gani ga duk wata qabila da ba ta shi ba. Amma a lokacin da mutum ya samu damar halartar makarantun gaba da jami’a, inda kusan kowacce qabila ta na da ‘ya ‘yanta a matsayin dalibai, bayan dogon lokacin da mutum zai dauka ya na karatu tare da mu’amala da mutane daga qabilu daban daban, za ka ga ya samu chanji a dabi’arsa daga qin jini ko gani – gani ga wasu qabilun da ba nashi ba.
Na hudu, dabi’ar mutum ne ke ba shi dama ya bayyanawa duniya ko shi wanene, dabi’arsa ce ke ba shi daman bayyana al’adarshi da irin halayenshi. Kamar misali, a shekarun baya da su ka shude a jihar Kano, idan ka ga mutum da jar hula, babu tantama wannan jar hula na alamta qauna ne ko shauqin Malam Aminu Kano. A yanzu kuma idan ka ga mutum da hula a Kano, mutane na saurin fassara shi ne da kasancewa dan Kwankwasiyya. Wannan ne ya sa da yawan dattawa (tsofaffi) a cikin garin Kano su ka watsar da jajayen hulunansu (Na Malam Aminu Kano) saboda su ba’yan kwankwasiyya ba ne, kuma ba su so a fassara su a haka.
Duk da dabi’a ba wata aba ba ce da a ke iya gani da ido, ko a taba, amma a na iya auna ta. Wannan ba sabon abu ba ne. idan ka na so ka fahimci inda dabi’ar mutum ta dosa dangane da wani al’amari bari ka ji yadda a ke auna dabi’a. Akwai wasu hanyoyin auna dabi’a da yawan gaske wadanda mu ke amfani da su, amma mafi sauqin ciki zan yi bayani a kai.
Kamar misali, ka na so ka fahimci shin menene ra’ayin mutum dangane da auren zawarawa da wasu gwamnoni ke bayarwa. Sai ka yi mishi tambaya kamar haka; Shin ka na goyon bayan auren zawaran da gwamnati ke jagoranta? Kai za ka qayyade amsoshin da mai amsawa zai zaba, ba wai za ka barshi ya yi ta zubo bayani ba ne. misali sai ka bashi zabi biyu; Eh ko A’a.
Duk amsar da wanda a ka tambaya ya zaba a cikin biyun, da su za ka auna dabi’arsa dangane da auren zawarawa. Idan ya zabi EH. Shi kenan ka gano cewa dabi’arsa dangane da auren zawarawa ta goyon baya ce, wannan zai sa ba za ka riqa fargabar yin maganan auren zawarawa da shi ba, musamman muhimmancinshi da kuma amfaninshi. Idan kuma ya zabi A’A, ya na nuna dabi’arsa ba ta qaunar auren zawarawan da a ke yi, shi zai sa ka kiyaye yawan matsawa a kan auren zawarawa a duk wata tattaunawarka ko mu’amalarka da wannan mutumin. Mu hadu mako mai zuwa
SAUYI A CIKIN AL’UMMA: NAZARIN BUKIN ZAGAYOWAR RANAR HAIHUWA (Birthday)
Kowanne mutum a duniya haifo shi a ka yi, babu wani tarihi da ya riske mu a kan cewa ga wani wanda shi fadowa ya yi daga sama, ba a jariri ba, da girmanshi da wayonshi. Wannan dalili na cewa kowanne mutum haihuwarsa a ka yi a duniya ne ya samar da ranar haihuwa.
A tsohuwar al’adar Malam Bahaushe, a ranar da a ka haifi mutum ba dole ba ne sai ya zama iyayenshi sun kiyaye kwanan wata da shekara, sai dai a kan yi wani abu mai ban sha’awa shi ne yi wa mutum lakabi da sunan ranar da a ka haife shi.
Wadanda a ka haifa a ranar Juma’a, a kan kirasu da Danjuma ko Danjummai, mace kuma a kira ta da Jummai ko Juma. Macen da a ka haifa ranar Laraba kuwa sunanta Balaraba, shi namijin Balarabe ko kuma Bala. Ranar litinin shi ne Dan liti, ranar Talata kuma dan tala.
Nazarin wadannan sunaye su ma abubuwa ne masu tasiri wanda su na da muhallinsu a ilmin sanin halayyar Jama’a.
Sauyi a cikin al’umma wani al’amari ne da ya zama wajibi, ba a iya kaucewa sauyi. Ko a na so ko ba a so ya na afkuwa. Kuma wani abun ban sha’awa da sauyi shi ne duk inda mutum ya je a fadin duniyar nan zai shaidi sauyin.
Haka kuma sauyi kan dauki salon faruwa a cikin karamin lokaci ko kuma lokaci mai tsawo. Wani al’ada na sauyi shi ne idan a ka samu sauyi a wani bangare na al’umma yak an shafi sauran bangarori.
Misali idan a ka samu sauyi a yanayin auratayya tsakanin mutane, wannan sauyi na iya shafar al’ada, idan sauyin da ya afku a yanayin auratayya ya afku ne ta fuskacin samuwar aure tsakanin kabilu mabambanta ba tare da la’akari da bambanci ba. Za a samu sauyi ne ta yanayin cakuduwar al’adu.
Wani sauyin mutane ne ke tsara shi yadda zai auku, wani kuma ya na aukuwa ne ba tare da sanin mutane ba. Misali, mutane kan sauya yanayin shigarsu (sanya tufafi) a lokacin da yanayin sanyi ya kankama. Sanyin ke takura mutum ya yi shigan da bai saba da it aba. A wuraren da dusar kankara ke sauka, sai ka ga wannan dusar ta tilasta musu yin wani irin shiga, wanda babu yadda wani a yankin da babu dusar ya yi irinta.
Cikin sauye sauyen da a ka samu a Nijeriya, mafi tasiri shi ne tasirin al’adar Bature a kasashen da ya mamaye a Afrika. Kamar a Nijeriya, an samu sauye sauye a yanayin zamantakewa; auratayya, buki, aiki (sana’o’i), tsarin abinci, sutura da sauransu.
Cikin kuskuren da Bature ya tafka a kasashen Afrika shi ne karfa karfan da ya yiwa kakanninmu wurin raba su da al’adunsu, ta hanyar shigo musu da nashi, tare da nuna musu al’adunshi a matsayin mafiya fifiko da dacewa ga rayuwar mutum.
Su ka fara sanyawa mutane dokokin tara iyali, kayyade haihuwa da auren mace guda daya rak, wai duk a sunan kiyaye bunkasar tattalin arzikin kasa. duk wannan bai kawar da mutanenmu 100% bisa 100% daga al’adunsu ba.
Amma zuwan zamani, musamman bayyanar al’amarin ‘Globalisation’ dunkulewar duniya wuri guda ya haifar da sauye sauye a al’ummu fiye da tsammani. A yanzu abun da ke faruwa a birnin Ingila, wanda ke zaune a kauyen Neja zai iya kallo kaitsaye, ko dai ta wayar salula ko ta yanar gizo a na’urar kwamfuta ko tashar talabijin.
Wannan ilmin sanin me ke faruwa a sassa daban daban na duniya ya taimaka wurin samun sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa. Ta yadda an jima a na kiyaye wacce rana a ka haifi mutum, wanne wata, a wacce shekara.
Don haka idan shekara ta zagayo, dai dai wannan ranar a cikin watan da a ka haifi mutum, akwai buki na musamman da a ke shiryawa na tunawa da wannan rana ta haihuwa, wasu yaran ma iyayensu ke shirya musu, har zuwa su girma su shiryawa kawunansu.
Al’adar bukin zagayowar ranar haihuwa, ba a kowacce al’ada ba ne akwai shi. Amma yanzu kuma ya zama a bu mafi wahalan gaske a rasa shi a cikin al’umma, komi kankanta akwai.
Ya zuwa yanzu ma sauyi ya sake bayyana a yanayin wannan murna na zagayowar ranar haihuwa a Nijeriya. Yadda masu dukiya ke wannan murnar ta bambanta da yadda talakawa ke yi, duk da ya ke talakawan na ta kokarin ko ta halin kaka sai sun kwaikwayi masu kudi, su kuma masu kudin hankoronsu sai sun kwaikwayi turawa.
A farko farkon bayyanar guguwar sauyin bukin zagayowar ranar haihuwa, yadda a ke taron shi ne a yi alkaki ‘cake’, ‘yan uwa da abokan arziki su taru, a yanka a ci, sannan a yi buki, masu bayar da kyauta ‘gift’ su bayar.
Wannan al’ada ce ta masu kudi, musamman a Nijeriya, idan su na aikata wani aiki talaka ya fara kwaikwayo, sai su yi kokarin yin kari ko sauya na su don a ga bambanci. Tunda talakawa ma na rufe ido su kwaikwaiyi yanka ‘cake’, sai kuma a ka samu sauyin fara yin babban buki, wanda za a ce ga kalan kayan da a ke so mahalarta su sanya, (misali, bakin wando da jar riga), sannan kuma a kama hayan wani babban otal wanda a can za a yi bukin.
Wannan sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa ya sa mata da yawa a yanzu na yin karyar ranar haihuwarsu, wata ma saboda kyaututtukan da samari kan kawo mata, ta kan shirya bukin zagayowar ranar haihuwa sau uku a shekara daya.
Mafi muhimmanci a yanzu ba wai kiyaye ranar haihuwar ba ne ma kawai, a’a bukin da ke cikin ranar a ke yi mawa, kyautar da za a samu a ke yi mawa, wanda a irin kyaututtukan wata har sabuwar mota fil a ke bata, wata kuma kudade. bukin dai ya zama jari. Toh ku taya ni murna da addu’a, nawa na gaske ne, ni ma ranar haihuwata ta zagayo. Mu hadu mako mai zuwa!
A tsohuwar al’adar Malam Bahaushe, a ranar da a ka haifi mutum ba dole ba ne sai ya zama iyayenshi sun kiyaye kwanan wata da shekara, sai dai a kan yi wani abu mai ban sha’awa shi ne yi wa mutum lakabi da sunan ranar da a ka haife shi.
Wadanda a ka haifa a ranar Juma’a, a kan kirasu da Danjuma ko Danjummai, mace kuma a kira ta da Jummai ko Juma. Macen da a ka haifa ranar Laraba kuwa sunanta Balaraba, shi namijin Balarabe ko kuma Bala. Ranar litinin shi ne Dan liti, ranar Talata kuma dan tala.
Nazarin wadannan sunaye su ma abubuwa ne masu tasiri wanda su na da muhallinsu a ilmin sanin halayyar Jama’a.
Sauyi a cikin al’umma wani al’amari ne da ya zama wajibi, ba a iya kaucewa sauyi. Ko a na so ko ba a so ya na afkuwa. Kuma wani abun ban sha’awa da sauyi shi ne duk inda mutum ya je a fadin duniyar nan zai shaidi sauyin.
Haka kuma sauyi kan dauki salon faruwa a cikin karamin lokaci ko kuma lokaci mai tsawo. Wani al’ada na sauyi shi ne idan a ka samu sauyi a wani bangare na al’umma yak an shafi sauran bangarori.
Misali idan a ka samu sauyi a yanayin auratayya tsakanin mutane, wannan sauyi na iya shafar al’ada, idan sauyin da ya afku a yanayin auratayya ya afku ne ta fuskacin samuwar aure tsakanin kabilu mabambanta ba tare da la’akari da bambanci ba. Za a samu sauyi ne ta yanayin cakuduwar al’adu.
Wani sauyin mutane ne ke tsara shi yadda zai auku, wani kuma ya na aukuwa ne ba tare da sanin mutane ba. Misali, mutane kan sauya yanayin shigarsu (sanya tufafi) a lokacin da yanayin sanyi ya kankama. Sanyin ke takura mutum ya yi shigan da bai saba da it aba. A wuraren da dusar kankara ke sauka, sai ka ga wannan dusar ta tilasta musu yin wani irin shiga, wanda babu yadda wani a yankin da babu dusar ya yi irinta.
Cikin sauye sauyen da a ka samu a Nijeriya, mafi tasiri shi ne tasirin al’adar Bature a kasashen da ya mamaye a Afrika. Kamar a Nijeriya, an samu sauye sauye a yanayin zamantakewa; auratayya, buki, aiki (sana’o’i), tsarin abinci, sutura da sauransu.
Cikin kuskuren da Bature ya tafka a kasashen Afrika shi ne karfa karfan da ya yiwa kakanninmu wurin raba su da al’adunsu, ta hanyar shigo musu da nashi, tare da nuna musu al’adunshi a matsayin mafiya fifiko da dacewa ga rayuwar mutum.
Su ka fara sanyawa mutane dokokin tara iyali, kayyade haihuwa da auren mace guda daya rak, wai duk a sunan kiyaye bunkasar tattalin arzikin kasa. duk wannan bai kawar da mutanenmu 100% bisa 100% daga al’adunsu ba.
Amma zuwan zamani, musamman bayyanar al’amarin ‘Globalisation’ dunkulewar duniya wuri guda ya haifar da sauye sauye a al’ummu fiye da tsammani. A yanzu abun da ke faruwa a birnin Ingila, wanda ke zaune a kauyen Neja zai iya kallo kaitsaye, ko dai ta wayar salula ko ta yanar gizo a na’urar kwamfuta ko tashar talabijin.
Wannan ilmin sanin me ke faruwa a sassa daban daban na duniya ya taimaka wurin samun sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa. Ta yadda an jima a na kiyaye wacce rana a ka haifi mutum, wanne wata, a wacce shekara.
Don haka idan shekara ta zagayo, dai dai wannan ranar a cikin watan da a ka haifi mutum, akwai buki na musamman da a ke shiryawa na tunawa da wannan rana ta haihuwa, wasu yaran ma iyayensu ke shirya musu, har zuwa su girma su shiryawa kawunansu.
Al’adar bukin zagayowar ranar haihuwa, ba a kowacce al’ada ba ne akwai shi. Amma yanzu kuma ya zama a bu mafi wahalan gaske a rasa shi a cikin al’umma, komi kankanta akwai.
Ya zuwa yanzu ma sauyi ya sake bayyana a yanayin wannan murna na zagayowar ranar haihuwa a Nijeriya. Yadda masu dukiya ke wannan murnar ta bambanta da yadda talakawa ke yi, duk da ya ke talakawan na ta kokarin ko ta halin kaka sai sun kwaikwayi masu kudi, su kuma masu kudin hankoronsu sai sun kwaikwayi turawa.
A farko farkon bayyanar guguwar sauyin bukin zagayowar ranar haihuwa, yadda a ke taron shi ne a yi alkaki ‘cake’, ‘yan uwa da abokan arziki su taru, a yanka a ci, sannan a yi buki, masu bayar da kyauta ‘gift’ su bayar.
Wannan al’ada ce ta masu kudi, musamman a Nijeriya, idan su na aikata wani aiki talaka ya fara kwaikwayo, sai su yi kokarin yin kari ko sauya na su don a ga bambanci. Tunda talakawa ma na rufe ido su kwaikwaiyi yanka ‘cake’, sai kuma a ka samu sauyin fara yin babban buki, wanda za a ce ga kalan kayan da a ke so mahalarta su sanya, (misali, bakin wando da jar riga), sannan kuma a kama hayan wani babban otal wanda a can za a yi bukin.
Wannan sauyi a yanayin bukin zagayowar ranar haihuwa ya sa mata da yawa a yanzu na yin karyar ranar haihuwarsu, wata ma saboda kyaututtukan da samari kan kawo mata, ta kan shirya bukin zagayowar ranar haihuwa sau uku a shekara daya.
Mafi muhimmanci a yanzu ba wai kiyaye ranar haihuwar ba ne ma kawai, a’a bukin da ke cikin ranar a ke yi mawa, kyautar da za a samu a ke yi mawa, wanda a irin kyaututtukan wata har sabuwar mota fil a ke bata, wata kuma kudade. bukin dai ya zama jari. Toh ku taya ni murna da addu’a, nawa na gaske ne, ni ma ranar haihuwata ta zagayo. Mu hadu mako mai zuwa!
ILLOLIN BANGAR SIYASA DA RIKICIN ZABE GA MATASA
Tabbas matasa na da muhimmancin gaske a kowacce al’umma, tasirinsu ya fi gaban a zura ido kawai ga al’amura ko yanayin yadda su ke gudanar da rayuwa. Wajibi ne da ya hau kan al’umma kan yin tattalin rayuwar matasa, samar da hanyoyin shigar da saqonnin abubuwa masu kyau don su siffantu da su, haka kuma a yi musu bayanin illolin abubuwa marasa kyau don su qaurace musu.
Duk wata qasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan ka waiwaiyi sirrin da ke tattare da samuwar wannan ci gaba, za ka ga a hannun matasansu ya ke. Saboda basu yin sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa.
Haqqi ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye da su kasance mataki na farko a inda ‘ya ‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin qasa da oda, kaucewa ayyukan barna da sauransu.
Idan iyaye su ka gaza aikata hakan ga ‘ya ‘yansu, babu tantama a dai dai lokacin da yaron ya kai shekarun girma (Matashi) ya fara mu’amala da wasu abokai a waje za su koya mishi dukkan dabi’un da su ka ga dama. A wasu lokutanma ba sai sun koya mishi ba, yanayin mu’amala a tsakaninshi da su ne zai sa ya riqa kwaikwaiyon yadda su ke tafiyar da rayuwarsu a hankali har ya gina dabi’a.
Wannan ya nuna cewa haqqin iyaye ne, kuma ikon kiyaye ‘ya ‘ya daga fadawa hadurran kwaikwayon halayen banza a waje na hannun iyayen ne. wanda idan a ka samu kaso 60% cikin 100% su na sauke wannan nauyi, za a ga chanji.
Qasashen da su ka ci gaba din nan, doka ce mai qarfi wacce ta tilasta iyaye a kan tarbiyyar ‘ya ‘yansu. Har ma idan iyayen ba su iya yi ba, sai hukuma ta dauki wannan babban aiki, saboda fahimtar irin hadarin da ke tattare da barin matasa cikin halin rashin bambance kyakkyawa da mummuna.
A qasashen Afrika, sai ya kasance kaso mai yawa na iyaye babu ruwansu da halin da ‘ya ‘yansu za su shiga idan har basu dauki nauyin kula da tarbiyyarsu ba. Haka kuma a wannan yanki namu na Afrika, iyaye da dama (sai dai kadan) ba su wani taka rawar a zo a gani wurin hobbasa kan ‘ya ‘yansu su yi karatu.
Halayen banza da aikata duk wani aiki da zai cutar da mutum ko ya janyo asarar dukiya ya na da alaqa da jahilci. Saboda shi jahilci babu abun da ya ke umurtar qwaqwalwa ta aikata face son rai da aiki ba tare da tantancewa tsakanin mai kyau da marar kyau ba.
Wannan shi ne dalilin da ya sa baragurbin ‘yan siyasa, wadanda ba burinsu ganin ci gaban Nijeriya ba, su ke amfani da matasa wurin cimma mummunar manufarsu ta aika aika. Su ne su ke ba matasan makamai da qwayoyi.
daya daga cikin abun da ke tashe a tsakankanin matasa a Nijeriya shi ne bangar siyasa da rikici. Wannan al’amari ya na da matuqar hadarin da idan ba an magance shi ba ne, lallai ba zai taba yiwuwa a mori dimokradiyya ko wanzajjen zaman lafiya ba.
A al’ummun da su ka ci gaba ba qaramin aibu bane a kira mutum da dan bangar siyasa ballantana kuma daya daga cikin masu hura wutar rikicin siyasa, amma a Nijeriya wannan ba komi ba ne. Wannan bangar siyasa ta bambanta da asalin ‘yan sara – suka da mu ke da su, da ‘yan kalare da ‘yan daba.
Duk inda a ka kira wadancan sunaye, musamman a garuruwan Bauchi, Kano da Gombe, suna ne wanda ya shafi matasa masu ayyukan rashin mutunci, rashin da’a da keta haqqoqin al’umma.
Zaben shekarar 1999, wanda tsohon janar, Olusegun Obasanjo ya lashe. Sai dai tun a wannan lokaci ne ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan rikicin zabe da bangar siyasa a tsakankanin matasa. Wannan irin mummunan dabi’a ta ci gaba da faruwa har a zaben shekarar 2003 da a ka yi. Maimakon a samu sauqe sai dai ma a ka yi ta samun qaruwar dabi’ar bangar siyasa da rikicin zabe ga matasa.
‘Yan siyasa masu mugun nufi a lokuta da dama su na aiki da matasan ne wurin sace akwatunan zabe, kai farmaki, da qone - qonen da su ka sabawa shari’a.
Yanayin da ke fuskantarmu, bisa la’akari da gabatowar babban zaben shekarar 2015, alamu na nuna matasan da ba su da ruwa da tsaki da da kalare, daba ko sara – suka akwai yiwuwar su fada ma irin wannan mummunan aiki na bangar siyasa da rikicin zabe.
A lokacin da a ka yi zaben fid da gwani na jam’iyyu a Nijeriya, an samu rahotannin yadda wasu ‘yan siyasa a jam’iyyun su ka yi amfani da matasa wurin tayar da hankula domin kawai su yi qaurin suna.
Ya kamata ne matasanmu su hankalta, su gane cewa bangar siyasa da rikicin zabe babu wani alheri da su ke haifarwa, sai dai sharruka birjik.
Rahotanni sun adana cewa a rikicin zaben shugaban qasa da ya auku a watan Afrilun 2011 ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 800, kamar yadda hukumar kare haqqin bil’adama su ka bayyana. Wadanda su ka mutu din an kashe su ne cikin kwanaki uku a jihohin arewa 11, wanda a kasha 90 na kashe – kashen matasa ne su ka aikata, haka ma rikicin zaben matasa ne su ka tayar.
Zaben shekarar 2011 da ya gabata ya tafi ya bar baya ta qura, bilhasali ma ba a taba yin zabe wanda a ka zubar da jinni kamar shi ba. An tarwatsa mutane daga muhallinsu, wasu sun rasa iyaye da ‘yan uwa. Hukumar bayar da tallafin gaggawa ta shaida cewa sama da mutane dubu 65,000 ne su ka bar gidajensu sakamakon rikicin.
Idan matasa su ka hankalta ta hanyar qauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas baragurbin ‘yan siyasa da basu son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga cimma burinsu ban a zubar jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
A matsayinka na matashi, ya kamata ne ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina rayuwarka, a samar da ayyukan da matasa za su yi bankwana da zaman banza, a samar musu guraben karatu a makarantun da mu ke da su; wannan shi ne aikin gina rayuwar mutum ba a bashi makami da qwaya ba. Makami da qwaya sai dai rusa rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da ka ke tare da su. Mu hadu mako mai zuwa!
Duk wata qasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan ka waiwaiyi sirrin da ke tattare da samuwar wannan ci gaba, za ka ga a hannun matasansu ya ke. Saboda basu yin sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa.
Haqqi ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye da su kasance mataki na farko a inda ‘ya ‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin qasa da oda, kaucewa ayyukan barna da sauransu.
Idan iyaye su ka gaza aikata hakan ga ‘ya ‘yansu, babu tantama a dai dai lokacin da yaron ya kai shekarun girma (Matashi) ya fara mu’amala da wasu abokai a waje za su koya mishi dukkan dabi’un da su ka ga dama. A wasu lokutanma ba sai sun koya mishi ba, yanayin mu’amala a tsakaninshi da su ne zai sa ya riqa kwaikwaiyon yadda su ke tafiyar da rayuwarsu a hankali har ya gina dabi’a.
Wannan ya nuna cewa haqqin iyaye ne, kuma ikon kiyaye ‘ya ‘ya daga fadawa hadurran kwaikwayon halayen banza a waje na hannun iyayen ne. wanda idan a ka samu kaso 60% cikin 100% su na sauke wannan nauyi, za a ga chanji.
Qasashen da su ka ci gaba din nan, doka ce mai qarfi wacce ta tilasta iyaye a kan tarbiyyar ‘ya ‘yansu. Har ma idan iyayen ba su iya yi ba, sai hukuma ta dauki wannan babban aiki, saboda fahimtar irin hadarin da ke tattare da barin matasa cikin halin rashin bambance kyakkyawa da mummuna.
A qasashen Afrika, sai ya kasance kaso mai yawa na iyaye babu ruwansu da halin da ‘ya ‘yansu za su shiga idan har basu dauki nauyin kula da tarbiyyarsu ba. Haka kuma a wannan yanki namu na Afrika, iyaye da dama (sai dai kadan) ba su wani taka rawar a zo a gani wurin hobbasa kan ‘ya ‘yansu su yi karatu.
Halayen banza da aikata duk wani aiki da zai cutar da mutum ko ya janyo asarar dukiya ya na da alaqa da jahilci. Saboda shi jahilci babu abun da ya ke umurtar qwaqwalwa ta aikata face son rai da aiki ba tare da tantancewa tsakanin mai kyau da marar kyau ba.
Wannan shi ne dalilin da ya sa baragurbin ‘yan siyasa, wadanda ba burinsu ganin ci gaban Nijeriya ba, su ke amfani da matasa wurin cimma mummunar manufarsu ta aika aika. Su ne su ke ba matasan makamai da qwayoyi.
daya daga cikin abun da ke tashe a tsakankanin matasa a Nijeriya shi ne bangar siyasa da rikici. Wannan al’amari ya na da matuqar hadarin da idan ba an magance shi ba ne, lallai ba zai taba yiwuwa a mori dimokradiyya ko wanzajjen zaman lafiya ba.
A al’ummun da su ka ci gaba ba qaramin aibu bane a kira mutum da dan bangar siyasa ballantana kuma daya daga cikin masu hura wutar rikicin siyasa, amma a Nijeriya wannan ba komi ba ne. Wannan bangar siyasa ta bambanta da asalin ‘yan sara – suka da mu ke da su, da ‘yan kalare da ‘yan daba.
Duk inda a ka kira wadancan sunaye, musamman a garuruwan Bauchi, Kano da Gombe, suna ne wanda ya shafi matasa masu ayyukan rashin mutunci, rashin da’a da keta haqqoqin al’umma.
Zaben shekarar 1999, wanda tsohon janar, Olusegun Obasanjo ya lashe. Sai dai tun a wannan lokaci ne ya kamata gwamnati ta tashi tsaye a kan rikicin zabe da bangar siyasa a tsakankanin matasa. Wannan irin mummunan dabi’a ta ci gaba da faruwa har a zaben shekarar 2003 da a ka yi. Maimakon a samu sauqe sai dai ma a ka yi ta samun qaruwar dabi’ar bangar siyasa da rikicin zabe ga matasa.
‘Yan siyasa masu mugun nufi a lokuta da dama su na aiki da matasan ne wurin sace akwatunan zabe, kai farmaki, da qone - qonen da su ka sabawa shari’a.
Yanayin da ke fuskantarmu, bisa la’akari da gabatowar babban zaben shekarar 2015, alamu na nuna matasan da ba su da ruwa da tsaki da da kalare, daba ko sara – suka akwai yiwuwar su fada ma irin wannan mummunan aiki na bangar siyasa da rikicin zabe.
A lokacin da a ka yi zaben fid da gwani na jam’iyyu a Nijeriya, an samu rahotannin yadda wasu ‘yan siyasa a jam’iyyun su ka yi amfani da matasa wurin tayar da hankula domin kawai su yi qaurin suna.
Ya kamata ne matasanmu su hankalta, su gane cewa bangar siyasa da rikicin zabe babu wani alheri da su ke haifarwa, sai dai sharruka birjik.
Rahotanni sun adana cewa a rikicin zaben shugaban qasa da ya auku a watan Afrilun 2011 ya yi sanadiyyar rasa rayuka sama da 800, kamar yadda hukumar kare haqqin bil’adama su ka bayyana. Wadanda su ka mutu din an kashe su ne cikin kwanaki uku a jihohin arewa 11, wanda a kasha 90 na kashe – kashen matasa ne su ka aikata, haka ma rikicin zaben matasa ne su ka tayar.
Zaben shekarar 2011 da ya gabata ya tafi ya bar baya ta qura, bilhasali ma ba a taba yin zabe wanda a ka zubar da jinni kamar shi ba. An tarwatsa mutane daga muhallinsu, wasu sun rasa iyaye da ‘yan uwa. Hukumar bayar da tallafin gaggawa ta shaida cewa sama da mutane dubu 65,000 ne su ka bar gidajensu sakamakon rikicin.
Idan matasa su ka hankalta ta hanyar qauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas baragurbin ‘yan siyasa da basu son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga cimma burinsu ban a zubar jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
A matsayinka na matashi, ya kamata ne ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina rayuwarka, a samar da ayyukan da matasa za su yi bankwana da zaman banza, a samar musu guraben karatu a makarantun da mu ke da su; wannan shi ne aikin gina rayuwar mutum ba a bashi makami da qwaya ba. Makami da qwaya sai dai rusa rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da ka ke tare da su. Mu hadu mako mai zuwa!
A SIYAR DA RAI A NEMO SUNA!
Haha! Matuqar ka na raye za ka yi gane – gane a duniyan nan, musamman idan ka na mu’amala da mutane barkatai, ko kuma ka na da ikon samun labarun yanayin yadda mutane daban daban daga sassan duniya su ke gudanar da rayuwarsu. A nan ne za ka tabbatarwa da kanka qarfin halin ‘yan neman suna.
Siyar da rai kala kala ne, kuma kusan masu irin wannan dabi’a ta siyar da rai sun san duk wata hanya da za su bi su aikata hakan, a wasu lokutan ta sha rutsawa da su, a wasu lokutan kuma su tsallake rijiya da baya.
Idan a ka ce siyar da rai kawai a ka yi shiru. Sai mutum ya dauka a na nufin a wurin siyar da ran dole sai ya kasance akwai barazana ga rayuwa. Wanda kuma ba haka ba ne, siyar da rai a nemo suna, ya na iya qumsar aikin da zai zubar da mutunci, qima, dattako ko ya rage kaifin wayonka a idon jama’a. wannan shi ne ma babban siyar da rai.
Wasu misalai na siyar da rai amma a ka samo sunan da a ke nema, shi ne irin qeqyashewa da tsayin dakan da tsohon mataimakin shugaban qasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi gab da zaben shekarar 2007. Inda ya fito kaitsaye ya yi fito na fito da muradin mai gidanshi, tsohon shugaban qasa Olusegun Obasanjo.
Siyar da ran da Atiku Abubakar ya yi, a na iya cewa ya ci riba, ya kuma yi suna sosai a wancan lokaci. Musamman yadda ‘yan Nijeriya su ka fara kallonshi a matsayin wani sabon gwarzo, wanda ya rusa sabuwar aqidar ‘Third Term’.
Atiku Abubakar bai tantance fada wa kasadar siyar da rai ba, har sai da ya samu tabbatattun hujjoji a kan maigidanshi Obasanjo ba zai tallafa mishi don ya maye gurbinshi ba. Sannan ya tabbatar da cewa idan har haqar ‘Third Term’’ ta cimma ruwa, shi kam sai dai kuma tarihi. Zabi biyu a wancan lokaci Alhaji Atiku Abubakar ke da su; ko dai ya danne zuciyarshi ya hadiyi haquri da duk wani wulaqanci da zai biyo baya. Ko kuma ya qaddamar da yaqi ba qaqqautawa.
A ‘yan kwanakin baya ma, siyar da ran da Malam Ibrahim Shekarau ya yi babban misali ne, saboda shi kanshi ya san ya siyar da rai ne a matakai biyu; komawa jam’iyyar PDP wacce a baya ya la’ance ta iya la’anta da abubuwan da za su biyo baya na kallon da jama’a za su riqa yi mishi. Na biyu shi ne ya zauna a cikin jam’iyyar adawa ta APC ma siyar da rai ne. bisa dalilin ita uwar jam’iyyar ta qasa ta shardanta cewa duk jihar da gwamna ko mataimakin gwamna ya komo jam’iyyar, shi ne zai zama shugabanta na jiha.
A halin da Malam Shekarau ya tsinci kanshi, ko dai ya zauna a cikin jam’iyyar ta APC qarqashin abokin adawanshi gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso ko kuma ya kama gabanshi (matakin da ya dauka). Qarshenta dai da Malam Ibrahim Shekarau ya duba da kyau, ya natsu ya ga cikin biyun, wanne siyar da rai ne zai zamar mishi mai sauqi sauqi.
Tsoron yin kasadar siyar da rai ne ya hana mutane irinsu Gwamna Sule Lamido, da Gwamna Babangida Aliyu su biye ma takwarrorinsu su Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko, Gwamna Kwankwaso da Gwamna Amaechi. Saboda ba su shirya ba, kar wurin neman suna su kwan ciki.
Wadannan su ne kadan daga cikin misalan siyar da rai a siyasance. Haka nan a mu’amalarmu ta yau da kullum, cike ta ke da siyar da rai. Musamman wadanda babban burinsu shi ne neman suna da son a ce su ne su ka yi kaza da kaza.
Wasu mutanen dabi’arsu kenan a ce su ne su ka fara aikata wani al’amari, ko su ne su ka dai daita wani abu, alhali ba za su yi nazarin me neman sunan nan zai iya janyo musu ba. Shin idan sun siyar da rai, qima da darajar da su ke kwadayi za su samu ko a’a?
Kowanne mutum mai hankali a duniyan nan, ya na da lura da kiyaye abubuwan da kan je kan dawo. Kawai yawancin abun da ke cutar da mutane a wannan zamani shi ne rashin tunani. Kyau a ce duk abun da ka riska ka tsaya ka yi tunani, ka yi nazari na musamman dangane da abun, ka tantance ka cire abubuwan da za su iya shafar mutuncinka ko qima, ko daraja, idan har akwai wadannan barazana masu yawa, sai ka yi haquri kawai.
Saboda mutunci shi ne mutum. Duk lokacin da kaso 40 cikin 100 na jama’an da ke kallonka da mutunci su ka daina, ina mai tabbatar maka da ka rasa wani babban abu a rayuwanka wanda zai yi ta janyo maka asarori na daukaka da amintan jama’a, har zuwa lokacin da za a sake sakankancewa da kai da al’amuranka.
Sau da yawa, ya fi kyautuwa ka yi shiru a abun da bai shafe ka ba. Wasu kan yi alqawuran siyar da rai, don kawai su farantawa mutum rai, alhali idan alqawarin bai cika ba, maimakon su nemo suna, sai dai su zubar da suna.
Daga qarshe ina kira ga masu dabi’ar siyar da rai don neman suna, su taimakawa kansu su rage, saboda ba kowanne siyar da ran ba ne ke tattare da suna. Wani maimakon nemo suna, sai dai ya janyo kuka da raunin da tabonshi ba zai taba gushewa ba. Mu hadu mako mai zuwa!
Siyar da rai kala kala ne, kuma kusan masu irin wannan dabi’a ta siyar da rai sun san duk wata hanya da za su bi su aikata hakan, a wasu lokutan ta sha rutsawa da su, a wasu lokutan kuma su tsallake rijiya da baya.
Idan a ka ce siyar da rai kawai a ka yi shiru. Sai mutum ya dauka a na nufin a wurin siyar da ran dole sai ya kasance akwai barazana ga rayuwa. Wanda kuma ba haka ba ne, siyar da rai a nemo suna, ya na iya qumsar aikin da zai zubar da mutunci, qima, dattako ko ya rage kaifin wayonka a idon jama’a. wannan shi ne ma babban siyar da rai.
Wasu misalai na siyar da rai amma a ka samo sunan da a ke nema, shi ne irin qeqyashewa da tsayin dakan da tsohon mataimakin shugaban qasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi gab da zaben shekarar 2007. Inda ya fito kaitsaye ya yi fito na fito da muradin mai gidanshi, tsohon shugaban qasa Olusegun Obasanjo.
Siyar da ran da Atiku Abubakar ya yi, a na iya cewa ya ci riba, ya kuma yi suna sosai a wancan lokaci. Musamman yadda ‘yan Nijeriya su ka fara kallonshi a matsayin wani sabon gwarzo, wanda ya rusa sabuwar aqidar ‘Third Term’.
Atiku Abubakar bai tantance fada wa kasadar siyar da rai ba, har sai da ya samu tabbatattun hujjoji a kan maigidanshi Obasanjo ba zai tallafa mishi don ya maye gurbinshi ba. Sannan ya tabbatar da cewa idan har haqar ‘Third Term’’ ta cimma ruwa, shi kam sai dai kuma tarihi. Zabi biyu a wancan lokaci Alhaji Atiku Abubakar ke da su; ko dai ya danne zuciyarshi ya hadiyi haquri da duk wani wulaqanci da zai biyo baya. Ko kuma ya qaddamar da yaqi ba qaqqautawa.
A ‘yan kwanakin baya ma, siyar da ran da Malam Ibrahim Shekarau ya yi babban misali ne, saboda shi kanshi ya san ya siyar da rai ne a matakai biyu; komawa jam’iyyar PDP wacce a baya ya la’ance ta iya la’anta da abubuwan da za su biyo baya na kallon da jama’a za su riqa yi mishi. Na biyu shi ne ya zauna a cikin jam’iyyar adawa ta APC ma siyar da rai ne. bisa dalilin ita uwar jam’iyyar ta qasa ta shardanta cewa duk jihar da gwamna ko mataimakin gwamna ya komo jam’iyyar, shi ne zai zama shugabanta na jiha.
A halin da Malam Shekarau ya tsinci kanshi, ko dai ya zauna a cikin jam’iyyar ta APC qarqashin abokin adawanshi gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso ko kuma ya kama gabanshi (matakin da ya dauka). Qarshenta dai da Malam Ibrahim Shekarau ya duba da kyau, ya natsu ya ga cikin biyun, wanne siyar da rai ne zai zamar mishi mai sauqi sauqi.
Tsoron yin kasadar siyar da rai ne ya hana mutane irinsu Gwamna Sule Lamido, da Gwamna Babangida Aliyu su biye ma takwarrorinsu su Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko, Gwamna Kwankwaso da Gwamna Amaechi. Saboda ba su shirya ba, kar wurin neman suna su kwan ciki.
Wadannan su ne kadan daga cikin misalan siyar da rai a siyasance. Haka nan a mu’amalarmu ta yau da kullum, cike ta ke da siyar da rai. Musamman wadanda babban burinsu shi ne neman suna da son a ce su ne su ka yi kaza da kaza.
Wasu mutanen dabi’arsu kenan a ce su ne su ka fara aikata wani al’amari, ko su ne su ka dai daita wani abu, alhali ba za su yi nazarin me neman sunan nan zai iya janyo musu ba. Shin idan sun siyar da rai, qima da darajar da su ke kwadayi za su samu ko a’a?
Kowanne mutum mai hankali a duniyan nan, ya na da lura da kiyaye abubuwan da kan je kan dawo. Kawai yawancin abun da ke cutar da mutane a wannan zamani shi ne rashin tunani. Kyau a ce duk abun da ka riska ka tsaya ka yi tunani, ka yi nazari na musamman dangane da abun, ka tantance ka cire abubuwan da za su iya shafar mutuncinka ko qima, ko daraja, idan har akwai wadannan barazana masu yawa, sai ka yi haquri kawai.
Saboda mutunci shi ne mutum. Duk lokacin da kaso 40 cikin 100 na jama’an da ke kallonka da mutunci su ka daina, ina mai tabbatar maka da ka rasa wani babban abu a rayuwanka wanda zai yi ta janyo maka asarori na daukaka da amintan jama’a, har zuwa lokacin da za a sake sakankancewa da kai da al’amuranka.
Sau da yawa, ya fi kyautuwa ka yi shiru a abun da bai shafe ka ba. Wasu kan yi alqawuran siyar da rai, don kawai su farantawa mutum rai, alhali idan alqawarin bai cika ba, maimakon su nemo suna, sai dai su zubar da suna.
Daga qarshe ina kira ga masu dabi’ar siyar da rai don neman suna, su taimakawa kansu su rage, saboda ba kowanne siyar da ran ba ne ke tattare da suna. Wani maimakon nemo suna, sai dai ya janyo kuka da raunin da tabonshi ba zai taba gushewa ba. Mu hadu mako mai zuwa!
MENENE TSORO?
Akwai wani lokaci da na je qauye a Arewacin Nijeriya, sai na yi niyyan siyan Kankana. Yayin da mai kankana ya zabo wata ‘yar babba, ya na so ya yanka, sai na lura wuqar ta yi datti sosai, na buqaci ya wanke ta tukunna. Ba tare da qyashi ba, ya tsuguna ya sa hannu a wani magudanan ruwa ya fara wanke wuqan, daga can nesa na hango yara da masu wucewa na tsayawa su tsula fitsari abunsu a magudanan ruwan.
Nan da nan na yi gaggawa na ce mishi, Malam ban ma so a yanka, kawai bani Kankanan a haka, ba tare da an yanka ba. Ina ganin wannan, wani zance na masana halayyar Jama’a ne ya fado min, inda su ke cewa, ‘Yayin da mutane su ke kallon abu a matsayin shi ne haqiqa, toh shi ne haqiqan a dukkan mu’amalolinsu.’
A dan wannan misali, mu na iya ganin yadda shi a wurin mai siyar da Kankana na qauye, bai yarda a haqiqa cewa akwai wasu qwayoyin cututtuka ba. Ni kuma da na zo daga birni na yi imanin cewa a haqiqanin gaskiya akwai qwayoyin cuta. Kuma kowanne dayya a cikinmu (tsakanina da mai kankana) mun yi aiki ne da yadda mu ka fahimci haqiqa.
Ba kawai wai ni ina da wayo ba ne ya sa na gaskata samuwar qwayoyin cututtuka, a’a, wannan ya na da alaqa da al’umman da na taso a cikinsu ne.
Wani qarin misali dangane da yadda mu ke kallon haqiqanin abu, shi ne misalin wasu tagawaye, masu suna Jack da Oscar, wadanda a ka yi rainonsu har zuwa girma a wurare daban daban. Jack an yi rainonshi a Trinidad shi kuma Oscar an raine shi a qasar Jamus.
Jack sai ya girma da qiyayyar Hitler a zuciyarshi, saboda a Trinidad ya taso. Yayin da dan uwanshi Oscar kuma ya girma da qaunar Hitler cike da zuciyanshi.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba wai abun da Hitler ya aikata ba ne asalin haqiqa. Haqiqa shi ne yadda mu ke kallon abun da shi Hitler din ya aikata.
Lokacin da a ka sace ‘yan matan makarantar Sakandare sama da 200 a garin Chibok. Yanayin yadda gwamnatin shugaban qasa Goodluck Jonathan ta riqi al’amarin ya na da fassarorida yadda kowanne mutum ko bangare na mutane za su kalle shi.
A garin Chibok da wasu yankunan Arewa, za a kalli wannan a matsayin sakaci daga shugaban qasa, saboda shi ke da ikon kiyaye duk wani dan qasa. Amma idan ka samu wani dan Neja Delta, zai iya ce ma ka babu laifi a banzantar da zancen da Shugaban Goodluck ya yi har na tsawon awanni 48, saboda bai yi imanin an sace su da gaske ba.
Masana halayyar Jama’a da zamantakewa (Sociologist) su na kiran irin wannan da yadda a ke kallo ko fassara haqiqanin al’amari. Al’umman da mu ka taso a cikinta ne ko dasa mana abubuwa da daman gaske, ciki har da yanayin yadda mu ke fahimtar haqiqanin abu. Ko mun sani ko ba mu sani ba, tasirin inda mu ka taso ne ke koyar da mu qin wani al’amari ko mutum, tare da son wani al’amari.
Wannan ba qaramin maudu’i ba ne, duk da wani na iya kallonshi a matsayin Kalmar ‘TSORO’ zalla, alhali al’amarin wuce nan.
Idan ka na so ka san menene haqinanin ma’anar tsoro, sai ka kalli Kalmar ta siffofi daban daban; idan kuwa har ka kalleta ta siffofi, za ka gamsu cewa babu wani ma’ana guda daya da ke daukan gundarin fassaran Kalmar ‘Tsoro’.
Misali, idan a ka ce abinci, ka ga ko ma dai menene, abun da ke fara zuwa a zuciyar duk wanda ya ji Kalmar shi ne, wani abu wanda zai iya yiwuwa ya shiga cikin mutum ya zauna, ko kuma ya shiga cikin a amayo shi.
Amma kawai idan a ka ce ma ka ‘Tsoro’, za ka buqaci a ba ka dama ka yi bayani, saboda shi ba yanayinsu daya da Kalmar ‘abinci’ ba. Sai a tambaye ka a ce ka fassara menene tsoro?. Ina mai tabbatar da cewa idan a ka yiwa mutum biyar wannan taambaya, amsoshinsu za su zama daban daban, amma idan ka tambaye su menene abinci, dole a amsarsu sai sun yi kamanni da juna.
Wani zai ce, tsoro shi ne firgita. Yayin da amsar wani za ta kasance, tsoro shi ne kidimewa. Wani amsan kuma na iya cewa tsoro shi ne fita daga hayyacin dai dai zuwa wani hayyaci na ba dai dai ba.
Toh idan haka ne, irin wadannan kalmomi, ta ya za mu iya fassara su ko kuma mu fahimce su yadda ya dace? Wannan ba wani abu ba ne mai wahala, ya na da sauqin gaske.
A wurin qananan Yara ‘yan qasa da shekaru 10, tsoro shi ne duk wani abu mai muni. Don haka ne ma za ka ga a lokuta da dama, irin Yaran nan masu qiriniya, sai ka ga iyayensu na ce musu ga ‘DODO’ nan. Ba wai Dodon ba ne da gaske, sannan ba wai kawai fadin Kalmar Dodon ba ne a baki, idan iyayen su k ace ga Dodo nan, sai su yi wani irin yamutse fuska ko su ma su yi wani irin firgigi yayin da su ke cewa dodon na zuwa.
Wannan yanayi da iyayen ke yi, shi ne yin tasiri a zukatan Yara, sai su gina tsoron dodo a zukatansu. Ka na iya gane tsoro a yanayin Yaro, yayin da yana yin wani abu, sai mahaifiyarshi ko mahaifinshi ya ce, ‘Ku kawo min Bulala’, a nan ba wai Kalmar bulalar b ace ke da tasiri, ta na iya yiwuwa an taba tsula ma yaron bulala, don haka qwaqwalwarshi ta kiyaye tsoron bulala.
Kaman ka kalli mutum geme – geme ne k ace mishi ga Dodo, kai ma ka san ka na batawa kanka lokaci ne. ko kuma ka kalli matashi wanda yah aura shekaru 20 zuwa sama (yana ganiyar balaga) don ya yi laifi ka ce a kawo bulala.
Tsoro a wurin matasa, shi ne kakkausan kalamai daga bakin iyayensu ko wasu wadanda su ke qimantawa. Za ka ga a lokuta da yawan gaske, idan wani abun firgici ya faru, za ka ji matashi na cewa, ‘Ni wallahi ban tsorata ba’, saboda shi a wurinshi, dar din da ya ji a cikin zuciyarshi ba sunanshi tsoro ba. Amma idan a ka kori matashi daga makarantar sakandare ko Jami’a, za ka ji ya na cewa, “Tsorona shi ne idan mahaifi ko mahaifiyata su ka sani”.
A qarshe ina so mu gane cewa, tsoro shi ne tsoro. Yadda ka fahimce shi a na ka tunanin, ya bambanta da yadda baturen Ingila ya fahimci shi. Mu hadu mako mai zuwa
Nan da nan na yi gaggawa na ce mishi, Malam ban ma so a yanka, kawai bani Kankanan a haka, ba tare da an yanka ba. Ina ganin wannan, wani zance na masana halayyar Jama’a ne ya fado min, inda su ke cewa, ‘Yayin da mutane su ke kallon abu a matsayin shi ne haqiqa, toh shi ne haqiqan a dukkan mu’amalolinsu.’
A dan wannan misali, mu na iya ganin yadda shi a wurin mai siyar da Kankana na qauye, bai yarda a haqiqa cewa akwai wasu qwayoyin cututtuka ba. Ni kuma da na zo daga birni na yi imanin cewa a haqiqanin gaskiya akwai qwayoyin cuta. Kuma kowanne dayya a cikinmu (tsakanina da mai kankana) mun yi aiki ne da yadda mu ka fahimci haqiqa.
Ba kawai wai ni ina da wayo ba ne ya sa na gaskata samuwar qwayoyin cututtuka, a’a, wannan ya na da alaqa da al’umman da na taso a cikinsu ne.
Wani qarin misali dangane da yadda mu ke kallon haqiqanin abu, shi ne misalin wasu tagawaye, masu suna Jack da Oscar, wadanda a ka yi rainonsu har zuwa girma a wurare daban daban. Jack an yi rainonshi a Trinidad shi kuma Oscar an raine shi a qasar Jamus.
Jack sai ya girma da qiyayyar Hitler a zuciyarshi, saboda a Trinidad ya taso. Yayin da dan uwanshi Oscar kuma ya girma da qaunar Hitler cike da zuciyanshi.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba wai abun da Hitler ya aikata ba ne asalin haqiqa. Haqiqa shi ne yadda mu ke kallon abun da shi Hitler din ya aikata.
Lokacin da a ka sace ‘yan matan makarantar Sakandare sama da 200 a garin Chibok. Yanayin yadda gwamnatin shugaban qasa Goodluck Jonathan ta riqi al’amarin ya na da fassarorida yadda kowanne mutum ko bangare na mutane za su kalle shi.
A garin Chibok da wasu yankunan Arewa, za a kalli wannan a matsayin sakaci daga shugaban qasa, saboda shi ke da ikon kiyaye duk wani dan qasa. Amma idan ka samu wani dan Neja Delta, zai iya ce ma ka babu laifi a banzantar da zancen da Shugaban Goodluck ya yi har na tsawon awanni 48, saboda bai yi imanin an sace su da gaske ba.
Masana halayyar Jama’a da zamantakewa (Sociologist) su na kiran irin wannan da yadda a ke kallo ko fassara haqiqanin al’amari. Al’umman da mu ka taso a cikinta ne ko dasa mana abubuwa da daman gaske, ciki har da yanayin yadda mu ke fahimtar haqiqanin abu. Ko mun sani ko ba mu sani ba, tasirin inda mu ka taso ne ke koyar da mu qin wani al’amari ko mutum, tare da son wani al’amari.
Wannan ba qaramin maudu’i ba ne, duk da wani na iya kallonshi a matsayin Kalmar ‘TSORO’ zalla, alhali al’amarin wuce nan.
Idan ka na so ka san menene haqinanin ma’anar tsoro, sai ka kalli Kalmar ta siffofi daban daban; idan kuwa har ka kalleta ta siffofi, za ka gamsu cewa babu wani ma’ana guda daya da ke daukan gundarin fassaran Kalmar ‘Tsoro’.
Misali, idan a ka ce abinci, ka ga ko ma dai menene, abun da ke fara zuwa a zuciyar duk wanda ya ji Kalmar shi ne, wani abu wanda zai iya yiwuwa ya shiga cikin mutum ya zauna, ko kuma ya shiga cikin a amayo shi.
Amma kawai idan a ka ce ma ka ‘Tsoro’, za ka buqaci a ba ka dama ka yi bayani, saboda shi ba yanayinsu daya da Kalmar ‘abinci’ ba. Sai a tambaye ka a ce ka fassara menene tsoro?. Ina mai tabbatar da cewa idan a ka yiwa mutum biyar wannan taambaya, amsoshinsu za su zama daban daban, amma idan ka tambaye su menene abinci, dole a amsarsu sai sun yi kamanni da juna.
Wani zai ce, tsoro shi ne firgita. Yayin da amsar wani za ta kasance, tsoro shi ne kidimewa. Wani amsan kuma na iya cewa tsoro shi ne fita daga hayyacin dai dai zuwa wani hayyaci na ba dai dai ba.
Toh idan haka ne, irin wadannan kalmomi, ta ya za mu iya fassara su ko kuma mu fahimce su yadda ya dace? Wannan ba wani abu ba ne mai wahala, ya na da sauqin gaske.
A wurin qananan Yara ‘yan qasa da shekaru 10, tsoro shi ne duk wani abu mai muni. Don haka ne ma za ka ga a lokuta da dama, irin Yaran nan masu qiriniya, sai ka ga iyayensu na ce musu ga ‘DODO’ nan. Ba wai Dodon ba ne da gaske, sannan ba wai kawai fadin Kalmar Dodon ba ne a baki, idan iyayen su k ace ga Dodo nan, sai su yi wani irin yamutse fuska ko su ma su yi wani irin firgigi yayin da su ke cewa dodon na zuwa.
Wannan yanayi da iyayen ke yi, shi ne yin tasiri a zukatan Yara, sai su gina tsoron dodo a zukatansu. Ka na iya gane tsoro a yanayin Yaro, yayin da yana yin wani abu, sai mahaifiyarshi ko mahaifinshi ya ce, ‘Ku kawo min Bulala’, a nan ba wai Kalmar bulalar b ace ke da tasiri, ta na iya yiwuwa an taba tsula ma yaron bulala, don haka qwaqwalwarshi ta kiyaye tsoron bulala.
Kaman ka kalli mutum geme – geme ne k ace mishi ga Dodo, kai ma ka san ka na batawa kanka lokaci ne. ko kuma ka kalli matashi wanda yah aura shekaru 20 zuwa sama (yana ganiyar balaga) don ya yi laifi ka ce a kawo bulala.
Tsoro a wurin matasa, shi ne kakkausan kalamai daga bakin iyayensu ko wasu wadanda su ke qimantawa. Za ka ga a lokuta da yawan gaske, idan wani abun firgici ya faru, za ka ji matashi na cewa, ‘Ni wallahi ban tsorata ba’, saboda shi a wurinshi, dar din da ya ji a cikin zuciyarshi ba sunanshi tsoro ba. Amma idan a ka kori matashi daga makarantar sakandare ko Jami’a, za ka ji ya na cewa, “Tsorona shi ne idan mahaifi ko mahaifiyata su ka sani”.
A qarshe ina so mu gane cewa, tsoro shi ne tsoro. Yadda ka fahimce shi a na ka tunanin, ya bambanta da yadda baturen Ingila ya fahimci shi. Mu hadu mako mai zuwa
DAN SANDA ABUN TSORO NE?
Mai karatu a wannan makon zan so in wayar da kawunanmu ne dangane da 'yan sanda da ayyukan su, za mu ta~o inda ke yiwa duk wani dan qasa na gari qaiqaiyi dangane da aikin dan sanda. Su ma na gari cikin ‘yan sandan za su qaru da fashin baqin.
Kalmar POLICE an samo ta ne daga kalmar POLITIA daga harshen Latin, su ma Latin sun samo POLITIA ne daga harshen GIRKA, domin a asali Girka sun kira Kalmar ne da POLIS.
Kafin a samar da tsarin aikin dan sanda a hukumance a wannan qasar ta mu, da ma can mu na da hanyoyin da kakanninmu su ke bi wurin samar da tsaro, kare rayuka, dukiyoyi da sauransu. Kamar misali a qasar hausa akwai DOGARAI, wadanda su ke aikin masu bayar da kariya ga Sarakuna, kuma su ke gudanar da aikin sintiri a cikin gari. A wancan lokacin SARKIN DOGARAI shi ne ke a matsayin shugaban jami'an tsaro. Cikin ayyukansu sun hada da amsar haraji, lalubowa da kuma horas da mai laifi, hana aukuwar barna da sauransu.
Haka nan kuma mutanen Masarautar SAYFAWA da su ka rayu KANEM BORNO su ma sun jima da tsarin aikin 'yan sanda a al'adance. TALBA shi ne sunan shugaban 'yan sintiri kuma alqalin alqalai a kotun MAI (sarki).
A yankin Yarabawa kuwa, yammacin Nijeriya, sunan jami'an tsaro kafin zuwan turawan mulkin mallaka sun hada da ILARI, EMESE, ko AGUNbEN su ne ke gudanar da duk wasu ayyukan 'yan sanda, ayyukansu sun yi kamanni da na DOGARAI a arewacin Nijeriya.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba bature mai jan kunne ba ne ya zo ma mutanenmu da aikin dan sanda, ba bature ba ne ya koyar da mu harkar tsaro, da tsaronmu ya zo ya same mu, sai dai ma muguntar gur~ata mana harkar tsaron da ya yi.
Zan dan ta~o yadda turawan mulkin mallaka su ka qirqiri 'yan sandan zamani, manufofin qirqirarsu da kuma sakamakon da mu ke gani har yau.
Ya na da kyau kowannenmu ya san da cewa jami'an 'yan sanda da mu ke da su a hukumance a Nijeriya, turawan mulkin mallaka ne su ka samar da su. Turawan sun fara ne da gina hukumar mutum 30 a shekarar 1861 a wurin da su ka kira 'LAGOS COLONY' wanda daga bisani wannan tsarin ya kutso yankin hausawa a shekarar 1879. A shekarar 1896 ne a ka qaddamar da jami'an 'yan sandan Legas.
A shekarar 1930 ne a ka samu hadewar jami'an 'yan sanda Arewa da na Kudu a ka samar da hukumar 'yan sanda ta qasa, kuma a ka yi mata hedikwata a Legas. A shekarar 1943 ne kuma turawan mulkin mallaka na birtaniya su ka rubutawa hukumar kundin tsari.
Na kawo wannan dan taqaitaccen tarihi ne don in yi sharar fagen yadda mai karatu zai fahimci rawar da Turawa su ka taka na samar da 'yan sanda a hukumance, kuma sun yi hakan ne ba wai don kakanninmu su ci moriyar harkar tsaro ba, ba sun yi ba ne don a kare rayuka da dukiyoyin iyayenmu.
Turawan sun kafa hukumar 'yan sanda ne saboda su samarwa kawunansu da tsaro da kariya, haka nan kuma sun kafa su ne don su riqa amfani da qarfinsu wurin danne mutane, ladabtar da wadanda ke yiwa dokokin bature kunnen qashi.
Wannan ya bamu ilmin gano dalilin da ya sa baturen mulkin mallaka ya kafa hukumar 'yan sanda, an kafa su ne su don su kare son rai da muradun mai mulki ko mai iko.
Ko da baturen mulkin mallaka ya ba Nijeriya wani abu wai shi 'yancin kai, sai ya bar wa hukumar da su ka gaje shi gadon hukumar 'yan sanda.
Shi ya sa masana da dama su na ganin cewa matuqar ana son a ga abun arziki a hukumar 'yan sandan Nijeriya, to a rushe tsarin da Bature ya assasa.
dan sanda ya kamata ne ya zama abokin kowa, ya zama mai hankali da natsuwa, ya zama mai sanin ya kamata. A halin yanzu dai akasin haka a ke gani a Nijeriya, a wasu lokutan ma sai ka ji ina ma za a riqa gwajin tabin hankali kafin a dauki mutum aikin tsaro? Saboda yadda ‘yan sanda a Nijeriya su ka dauki sakar wuta kamar kwankwadan kofin ruwa.
Bai kamata dan sanda ya zama mai girman kai, mugunta, da zafi ga jama'a ba, saboda da kudin al'umma a ke tufatar da su, a ke biyansu albashi, don su zama masu bayar da kariya ta kowacce siffa ga ‘yan qasa, ka ga kenan su hadimai ne ba su zama dodanni ba.
Idan a na son haifar da da mai ido a qoqarin samar da fahimtar juna tsakanin yan sanda da mutanen gari, dole ne a shigo da harkar 'POLICE COMMUNITY RELATIONS', ma'ana gina kyakkyawar alaqa a tsakani. Mu hadu mako mai zuwa
Kalmar POLICE an samo ta ne daga kalmar POLITIA daga harshen Latin, su ma Latin sun samo POLITIA ne daga harshen GIRKA, domin a asali Girka sun kira Kalmar ne da POLIS.
Kafin a samar da tsarin aikin dan sanda a hukumance a wannan qasar ta mu, da ma can mu na da hanyoyin da kakanninmu su ke bi wurin samar da tsaro, kare rayuka, dukiyoyi da sauransu. Kamar misali a qasar hausa akwai DOGARAI, wadanda su ke aikin masu bayar da kariya ga Sarakuna, kuma su ke gudanar da aikin sintiri a cikin gari. A wancan lokacin SARKIN DOGARAI shi ne ke a matsayin shugaban jami'an tsaro. Cikin ayyukansu sun hada da amsar haraji, lalubowa da kuma horas da mai laifi, hana aukuwar barna da sauransu.
Haka nan kuma mutanen Masarautar SAYFAWA da su ka rayu KANEM BORNO su ma sun jima da tsarin aikin 'yan sanda a al'adance. TALBA shi ne sunan shugaban 'yan sintiri kuma alqalin alqalai a kotun MAI (sarki).
A yankin Yarabawa kuwa, yammacin Nijeriya, sunan jami'an tsaro kafin zuwan turawan mulkin mallaka sun hada da ILARI, EMESE, ko AGUNbEN su ne ke gudanar da duk wasu ayyukan 'yan sanda, ayyukansu sun yi kamanni da na DOGARAI a arewacin Nijeriya.
Wannan ya nuna mana cewa ashe ba bature mai jan kunne ba ne ya zo ma mutanenmu da aikin dan sanda, ba bature ba ne ya koyar da mu harkar tsaro, da tsaronmu ya zo ya same mu, sai dai ma muguntar gur~ata mana harkar tsaron da ya yi.
Zan dan ta~o yadda turawan mulkin mallaka su ka qirqiri 'yan sandan zamani, manufofin qirqirarsu da kuma sakamakon da mu ke gani har yau.
Ya na da kyau kowannenmu ya san da cewa jami'an 'yan sanda da mu ke da su a hukumance a Nijeriya, turawan mulkin mallaka ne su ka samar da su. Turawan sun fara ne da gina hukumar mutum 30 a shekarar 1861 a wurin da su ka kira 'LAGOS COLONY' wanda daga bisani wannan tsarin ya kutso yankin hausawa a shekarar 1879. A shekarar 1896 ne a ka qaddamar da jami'an 'yan sandan Legas.
A shekarar 1930 ne a ka samu hadewar jami'an 'yan sanda Arewa da na Kudu a ka samar da hukumar 'yan sanda ta qasa, kuma a ka yi mata hedikwata a Legas. A shekarar 1943 ne kuma turawan mulkin mallaka na birtaniya su ka rubutawa hukumar kundin tsari.
Na kawo wannan dan taqaitaccen tarihi ne don in yi sharar fagen yadda mai karatu zai fahimci rawar da Turawa su ka taka na samar da 'yan sanda a hukumance, kuma sun yi hakan ne ba wai don kakanninmu su ci moriyar harkar tsaro ba, ba sun yi ba ne don a kare rayuka da dukiyoyin iyayenmu.
Turawan sun kafa hukumar 'yan sanda ne saboda su samarwa kawunansu da tsaro da kariya, haka nan kuma sun kafa su ne don su riqa amfani da qarfinsu wurin danne mutane, ladabtar da wadanda ke yiwa dokokin bature kunnen qashi.
Wannan ya bamu ilmin gano dalilin da ya sa baturen mulkin mallaka ya kafa hukumar 'yan sanda, an kafa su ne su don su kare son rai da muradun mai mulki ko mai iko.
Ko da baturen mulkin mallaka ya ba Nijeriya wani abu wai shi 'yancin kai, sai ya bar wa hukumar da su ka gaje shi gadon hukumar 'yan sanda.
Shi ya sa masana da dama su na ganin cewa matuqar ana son a ga abun arziki a hukumar 'yan sandan Nijeriya, to a rushe tsarin da Bature ya assasa.
dan sanda ya kamata ne ya zama abokin kowa, ya zama mai hankali da natsuwa, ya zama mai sanin ya kamata. A halin yanzu dai akasin haka a ke gani a Nijeriya, a wasu lokutan ma sai ka ji ina ma za a riqa gwajin tabin hankali kafin a dauki mutum aikin tsaro? Saboda yadda ‘yan sanda a Nijeriya su ka dauki sakar wuta kamar kwankwadan kofin ruwa.
Bai kamata dan sanda ya zama mai girman kai, mugunta, da zafi ga jama'a ba, saboda da kudin al'umma a ke tufatar da su, a ke biyansu albashi, don su zama masu bayar da kariya ta kowacce siffa ga ‘yan qasa, ka ga kenan su hadimai ne ba su zama dodanni ba.
Idan a na son haifar da da mai ido a qoqarin samar da fahimtar juna tsakanin yan sanda da mutanen gari, dole ne a shigo da harkar 'POLICE COMMUNITY RELATIONS', ma'ana gina kyakkyawar alaqa a tsakani. Mu hadu mako mai zuwa
Subscribe to:
Posts (Atom)